Duniya Labari: Sanata a Najeriya Ya Riga Mu Gidan Gaskiya bayan Ya Shiga APC
- Majalisar dattawan Najeriya ta sake shiga jimami bayan sake rasa daya daga cikin mambobinta da ya yi bankwana da duniya
- Majiyoyi sun tabbatar da cewa Sanatan Rivers ta Kudu maso Gabas ya rasu yana da shekaru 64 bayan jinya
- An sanar da rasuwarsa a zaman kwamitin majalisar dattawa a yau Alhamis 19 ga watan Fabrairun shekarar 2026 da muke ciki
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Port Harcourt, Rivers - Majalisar dattawan Najeriya ta sake yin rashi bayan sanar da rasuwar daya daga cikin mambobinta.
An tabbatar da cewa sanatan da ke wakiltar mazabar Rivers ta Kudu maso Gabas a Majalisar Dattawa, Barinada Mpigi, ya rasu.

Source: Twitter
Rahotanni sun ce Mpigi, wanda shi ne shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Ayyuka, ya mutu yana da shekaru 64 bayan ya sha fama da rashin lafiya na wani lokaci, cewar Punch.
A watannin baya-bayan nan, mataimakin shugaban kwamitin ayyuka, Rufai Hanga, ne ya rika jagorantar wasu tarukan kwamitin ciki har da zaman kare kasafin kudi.
An sanar da rasuwar tasa ne a ranar Alhamis yayin zaman kare kasafin kudin Kwamitin Majalisar Dattawa kan Al’adu, Fasaha da Tattalin Arzikin Kirkire-kirkire.
Shugaban kwamitin, Ogwoshi Onawo, ne ya bayyana labarin rasuwar a gaban ‘yan kwamitin.
Bayan sanarwar, mambobin kwamitin sun tsayar da minti guda domin karrama marigayin.
An san Mpigi a matsayin daya daga cikin manyan ‘yan siyasa masu tasiri a jihar Rivers, musamman saboda kusancinsa da jama’a da kuma gina karfin siyasa daga tushe.
Kafin rasuwarsa, yana daga cikin sanatocin Rivers da suka sauya sheka daga jam’iyyar adawa ta PDP zuwa jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya.
Karin bayani na tafe....
Dan majalisar tarayya daga jihar Oyo, Oloye Akin Alabi ya tabbatar da labarin rasuwar sanata a wani rubutu da ya yi a shafin X.
Alabi, a cikin wani sako da ya wallafa a kafar sada zumunta, ya yi alhinin rasuwar sanatan Rivers tare da tuna cewa “shi ne Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Ayyuka.”
Wasu ‘yan Najeriya sun yi tururuwa zuwa sashen sharhi na sakon dan majalisar wakilan domin nuna alhininsu tare da yi wa marigayin addu’a.
Sanatan Najeriya ya rasu a Birtaniya bayan jinya
A wani labarin, Najeriya ta yi babban rashi bayan da aka sanar da mutuwar sanata mai ci wanda ya bar duniya bayan fama da jinya a kasar Birtaniya.
Sanata Okey Ezea daga Enugu ta Arewa ya rasu a kasar lamarin da ya girgiza jam’iyyar LP da mutanen yankinsa duba da gudunmawar da yake ba su.
Ezea shi ne ɗan majalisa guda kaɗai da ya ragewa LP daga Enugu, abin da ya sa rashin nasa ya fi ɗaga hankalin jama’a da yan mazabarsa baki daya.
Asali: Legit.ng

