Manyan Jam'iyyar APC da aka Gani Wajen Tarbar Gwamna Abba daga NNPP a Kano
Manyan shugabannin jam’iyyar APC ne suka hallara a Kano a ranar Litinin, 15 ga watan Fabrairu, 2026 inda suka karɓi gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf zuwa jam'iyya mai mulki.
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Jihar Kano - Jam'iyyar APC ta yi maraba da Abba Kabir Yusuf a hukumance cikin jam’iyyar a wani babban gangami da aka gudanar a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano a ranar Litinin.

Source: Facebook
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya shiga APC
Daily Trust ta wallafa cewa taron ya jawo dimbin magoya bayan jam’iyya da masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa daga sassa daban-daban na ƙasar nan.
Daga cikin wadanda suka halarci taron, akwai gwamnoni da sauran jiga-jigan APC da suka bayyana jin dadin sauya shekar gwamnan.
Legit ta tattaro sunayen wasu daga cikin manyan APC da suka halarci taron yi wa Gwamna Abba Kabir Yusuf lale zuwa jam'iyyar, sun hada da:
Kusoshin da aka gani wajen karbar Abba a APC
1. Mataimakin Shugaban kasa, Kashim Shettima
2. Mataimakin Shugaban majalisar dattawa, Barau I Jibril
3. Shugaban APC, Farfesa Nentawe Yilwatda
4.Shugaban majalisar Wakilai, Rt. Hon. Tajudden Abbas
5. Gwamna Hope Uzodinma
6. Gwamna Nasir Idris
7. Gwamna Umar Namadi
8. Gwamna Uba Sani
9.Gwamna Ahmad Aliyu
10. Mataimakin Gwamnan Katsina, Farouk Jobe
11. Tsohon Shugaban APC, Abdullahi Umar Ganduje
12. Atiku Bagudu Abubakar
13. Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Nasiru Gawuna
14. Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan Kano, Murtala Garo
15. Tsohon dan takarar gwamnan Kano, A. A Zaura
16. Sanata Kabiru Gaya
17. Sanata Kawu Sumaila
18. Tsohon Shugaban majalisar dattawa, Ovie Omo-Agege
19. 'Dan majalisar tarayya, Abba Bichi
20. Shugaban APC na Kano, Abdullahi Abbas
21. Baffa Babba Dan Agundi
22. Tsohon Gwamna Badaru Abubakar
Abin da Abba ya ce a taron APC
A yayin taron, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa sauya shekar zai taimaka wajen tabbatar da ci gaban Kano.
Ya bayyana cewa sauya shekarsa zai yi amfani, kuma a yanzu haka Kano ta shiga sahun masu fada a ji a gwamnatin tarayyar Najeriya.
Dangane da raba hanya da NNPP, Abba ya danganta ficewarsa daga jam'iyyar da rikice-rikicen cikin gida da kuma yawaitar shari’o’i.
Ya jaddada cewa da suka koma APC, Kano za ta ci gaba da samun tagomashi da ci gaba mai dorewa da za a samo daga gwamnatin tarayya.
Kashim ya fadi muhimmancin Kano ga APC
A wani labarin, kun ji cewa Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana jihar a matsayin muhimmin ginshiƙi ga nasarar jam’iyyar a matakin ƙasa da jiha.
Ya bayyana haka ne a ranar Litinin, 16 ga watan Fabrairu 2026 a lokacin da ya hadu da sauran shugabannin APC wajen karbar Gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa jam'iyyar.
A wajen taron, ya yabawa gwamna Abba da sauran shugabannin siyasa da suka yi wa APC biyayya, ciki har da ‘yan majalisun jiha 22, ‘yan majalisar tarayya takwas.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

