'Masu Tunanin 'Yan Arewa ba Za Su Zabi Tinubu a 2027 ba Sun Tafka Babban Kuskure'

'Masu Tunanin 'Yan Arewa ba Za Su Zabi Tinubu a 2027 ba Sun Tafka Babban Kuskure'

  • Tsohon shugaban APC na kasa, Abdullahi Ganduje ya ce babu wanda ya dace mutane su sake zaba a 2027 kamar Bola Ahmed Tinubu
  • Ganduje ya ce masu tunanin cewa 'yan Arewa za su juyawa Shugaba Bola Tinubu baya a zabe mai zuwa sun tafka babban kuskure
  • Tsohon gwamnan Kano ya fadi haka ne lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin matasa daga jihohin Arewa 19 a birnin tarayya Abuja

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na Kasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa wadanda ke tunanin cewa 'yan Arewa ba za su sake zaben Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba a 2027 suna "tafka babban kuskure."

Ganduje ya fadi hakan ne a ranar Juma’a a birnin Abuja, lokacin da shugabannin matasan Arewa daga jihohi 19 suka kai masa ziyarar ban girma domin nada shi a matsayin uban kungiyarsu.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Kano: Binciken Ganduje na nan duk da Abba ya shigo jam'iyyar APC

Ganduje.
Tsohon shugaban APC na kasa, Dr. Abdullahi Ganduje Hoto: Dr. Abdullahi Umar Ganduje
Source: Facebook

A rahoton Daily Trust, tohon gwamnan jihar Kano ya ce babu wani dan takara da ya fi dacewa ya mulki Najeriya bayan 2027 daga Kudancin Najeriya kamar Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.

Ya kara da cewa Najeriya ta yi sa’ar samun "ainihin dan siyasa" mai kishin kasa a matsayin shugaba.

Jawabin Abdullahi Ganduje kan zaben 2027

Game da zabe mai zuwa na 2027, Ganduje ya ce:

"Dangane da zabe mai zuwa na 2027, wadanda ke raya wa kansu ko tunanin cewa Arewa za ta zabi wani dan takara daban ba Asiwaju ba, sun tafka babban kuskure."
"Wannan ne karon farko da Najeriya ta yi sa’ar samun dan siyasa nagari a matsayin Shugaban Kasa. Siyasa ce tushensa, kuma a cikinta aka raine shi saboda ya yi imani da hadin kan kasar nan.
"Ma'ana dai ya sha gwagwarmaya, har gudun hijira ya tafi domin ganin dorewar dimokuradiyya a Najeriya. Don haka, babu wanda ya fi dacewa a zaba a 2027 sama da Bola Ahmed Tinubu."

Kara karanta wannan

'Dalilin da zai sa yankin Arewa ya yi wa Tinubu ruwan kuri'u a zaben 2027'

Yarjejeniyar da aka yi kafin zaben Buhari

Ganduje ya tunatar da cewa an yi yarjejeniya tun kafin zaben marigayi Shugaba Muhammadu Buhari cewa bayan shekaru takwas na mulkinsa, mulki zai koma Kudu, in ji Vanguard.

Ya bayyana cewa ko da yake Asiwaju bai kai shekaru hudu a kan mulki ba, an ga matakan garambawul da ya dauka domin inganta tattalin arziki da jin dadin jama'a.

Shugaban kasa, Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu tare da wasu gwamnonin APC a wurin kaddamar da aiki a Nasarawa Hoto: Abdullahi Sule
Source: Twitter

Ganduje ya kuma jinjina wa shugabannin matasan Arewan saboda jajircewarsu, ba wai kawai wajen tara kuri’u ba, har ma da shirin tara kudi domin sayan fom din takarar Asiwaju.

"Babu wata sadaukarwa da ta wuce wannan; kuna ba da kudi, kuna ba da tunaninku, kuna ba da karfinku, sannan kuna ba da lokacinku domin tabbatar da tazarcen Asiwaju. Dole ne mu gode muku kan wannan aiki," in ji Ganduje.

Matasan Arewa na tare da Tinubu

A wani labarin, kun ji cewa Kungiyar Matasan Arewa (NYF) ta yi magana kan tazarcen shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a zaben shekarar 2027.

Kara karanta wannan

Gwamna Abba ya kara samun karbuwa a APC awanni 24 bayan ya shiga jam'iyyar

Kungiyar ta bayyana cewa Arewa za ta mara wa Shugaba Tinubu baya domin ya sake samun wa’adi na biyu a zaben shugaban kasar 2027.

Matasan sun danganta matsayar ta da sauye-sauyen da Shugaba Tinubu ke aiwatarwa da jajircewarsa wajen tabbatar da haɗin kan ƙasa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262