‘Abin da Zai Hana Musulmi ’Yan Arewa Zaben Shugaban Kasa’: Jigon APC Ya Yi Gargadi
- Jigo a jam'iyyar APC, Farouk Aliyu, ya bayyana abin da yake ganin zai zabe saboda rashin jin daɗin tikitin shugaban ƙasa
- Ya ce yawan Musulmi a Arewa ne ke yanke makomar siyasa, inda ya gargadi APC kan illar sauya Musulmi da Kirista a zabe
- Aliyu ya jaddada cewa rikicin tikitin Musulmi–Musulmi na 2023 ya lafa, kuma ba a nuna fifiko ga Musulmi a mulkin Bola Tinubu ba
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja – Wani babban jigo a jam’iyyar APC a Arewa maso yammacin Najeriya, Farouk Aliyu, ya yi magana game da zaben 2027 da kuma tikitin Musulmi da Musulmi.
Kusan a APC ya ce yankin Arewa ba zai ji daɗin tikitin shugaban ƙasa da mataimaki Kirista da Kirista ba, yana mai gargadin cewa hakan na iya jefa jam’iyyar cikin matsala.

Source: Twitter
Jigon APC ya yi gargadi kan sauya Shettima
Aliyu ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin wata hira da ya yi a gidan talabijin na ARISE TV da aka wallafa a Youtube inda yake mayar da martani kan muhawarar ko APC za ta ci gaba da tikitin Musulmi–Musulmi.
Da yake dogaro da yanayin yawan jama’a a Arewa, jigon na APC ya ce jam’iyyar za ta yi la’akari da ƙididdigar yawan masu zaɓe wajen yanke shawarar irin tikitin da za ta fitar.
Ya ce:
“A gani na, za a duba yawan mutane ne wajen tantance ko za a tsayar da Musulmi ko Kirista, lambobin suna nan a fili.”
Farouk Aliyu ya ƙara da cewa babu shakka Musulmi sun fi yawa a Arewa, inda ya ce duk jam’iyyar da ke son cin nasara dole ta yi la’akari da haka.
Ya gargadi APC cewa sauya ɗan takara Musulmi da Kirista a Arewa na iya janyo wa jam’iyyar ƙalubale a zaɓe.

Kara karanta wannan
Juyin mulki: Ministan tsaro ya faɗi hukuncin da ke jiran sojojin, ya yi albishir ga iyalansu
“Ko a Arewa akwai Musulmi fiye da Kiristoci, babu shakka hakan gaskiya ne. Don haka jam’iyya na iya tsayar da Kirista, amma idan aka duba yawan jama’a, Musulmi sun fi yawa a Arewa, kuma hakan ne mafi alheri ga jam’iyyar ta tsayar da Musulmi.
“Tabbas, idan ka cire Musulmi ka saka Kirista a Arewa, za a shiga matsala."
- Farouk Aliyu

Source: Twitter
'Ba a yi wa Kiristoci wariya'
Aliyu ya kuma ce ce-ce-ku-cen da suka biyo bayan tikitin Musulmi–Musulmi a 2023 sun riga sun lafa, yana mai jaddada cewa Kiristoci ba sa fuskantar wariya a ƙarƙashin gwamnatin Shugaba Tinubu.
Ya ce:
“Wannan gwamnati ba ta da wani abin da za a nuna cewa tana fifita Musulmi a kan Kiristoci, don haka ina ganin tikitin Musulmi–Musulmi har yanzu na iya yin tasiri a APC.
“Dangane da Arewar da na sani, Arewa ba za ta ji daɗin tikitin Kirista–Kirista ba, domin idan aka yi haka, za a ware Musulmi gaba ɗaya a Arewa."
Wani matashin dan siyasa ya magantu
Kwamred Muhammad Sani One Day ya fadawa wakilin Legit Hausa cewa mafi yawan mutane sun waye ba su bukatar shawara kan yan takara.
Ya ce:
"A yanzu bai kamata a rika kawo mana maganar addini ko kabilanci cikin lamarin siyasa ba saboda ba shi da wani amfani.
"Da aka zabi Muslim/Muslim wane fa'ida Musulmi suka samu? babu wani bamabanci wani lokaci ma ana cewa Kiristoci sun fi jin dadin mulkin."
'Yan APC sun yi gargadi kan sauya Shettima
A wani labarin, an ji Kungiyar APC Youth Parliament North East ta yi karin haske game da jita-jitar da ake yadawa kan maganar sauya Kashim Shettima.
Shugaban kungiyar, Kabiru Garba Kobi daga Bauchi, ya zargi wasu 'yan siyasa da yada rade-radin saboda cimma burinsu.
Kabiru Kobi ya bayyana haka yayin da yake nuna damuwa game da jita-jitar sauya Shettima a ranar Lahadi 25 ga watan Janairun 2026 da muke ciki.
Asali: Legit.ng

