‘Abin da Zai Hana Musulmi ’Yan Arewa Zaben Shugaban Kasa’: Jigon APC Ya Yi Gargadi

‘Abin da Zai Hana Musulmi ’Yan Arewa Zaben Shugaban Kasa’: Jigon APC Ya Yi Gargadi

  • Jigo a APC, Farouk Aliyu, ya bayyana abin da yake ganin zai zabe saboda rashin jin daɗin tikitin shugaban ƙasa
  • Ya ce yawan Musulmi a Arewa ne ke yanke makomar siyasa, inda ya gargadi APC kan illar sauya Musulmi da Kirista
  • Aliyu ya jaddada cewa rikicin tikitin Musulmi–Musulmi na 2023 ya lafa, kuma ba a nuna fifiko ga Musulmi a mulkin Bola Tinubu ba

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja – Wani jigo a jam’iyyar APC, Farouk Aliyu, ya yi magana game da zaben 2027 da kuma tikitin Musulmi da Musulmi.

Kusa a APC ya ce yankin Arewa ba zai ji daɗin tikitin shugaban ƙasa da mataimaki Kirista da Kirista ba, yana mai gargadin cewa hakan na iya jefa jam’iyyar cikin matsala.

Jigon APC ya fadi tasirin tikitin Musulmi da Musulmi
Shugaba Bola Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Twitter

Jigon APC ya yi gargadi kan sauya Shettima

Kara karanta wannan

Buba Galadima ya kawar da NNPP, ya faɗi jam'iyyar da za ta kayar da Tinubu a 2027

Aliyu ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin wata hira da ya yi a gidan talabijin na ARISE TV da aka wallafa a Yutube inda yake mayar da martani kan muhawarar ko APC za ta ci gaba da tikitin Musulmi–Musulmi.

Da yake dogaro da yanayin yawan jama’a a Arewa, jigon na APC ya ce jam’iyyar za ta yi la’akari da ƙididdigar yawan masu zaɓe wajen yanke shawarar irin tikitin da za ta fitar.

Ya ce:

“A ganina, za a duba yawan mutane ne wajen tantance ko za a tsayar da Musulmi ko Kirista, lambobin suna nan a fili.”

Farouk Aliyu ya ƙara da cewa babu shakka Musulmi sun fi yawa a Arewa, inda ya ce duk jam’iyyar da ke son cin nasara dole ta yi la’akari da haka.

Ya gargadi APC cewa sauya ɗan takara Musulmi da Kirista a Arewa na iya janyo wa jam’iyyar ƙalubale a zaɓe.

“Ko a Arewa akwai Musulmi fiye da Kiristoci, babu shakka hakan gaskiya ne. Don haka jam’iyya na iya tsayar da Kirista, amma idan aka duba yawan jama’a, Musulmi sun fi yawa a Arewa, kuma hakan ne mafi alheri ga jam’iyyar ta tsayar da Musulmi.

Kara karanta wannan

APC na shirin mamaye Najeriya, bayan Abba, wasu gwamnoni za su sauya sheka

“Tabbas, idan ka cire Musulmi ka saka Kirista a Arewa, za a shiga matsala."

- Farouk Aliyu

Jigon APC ya fadi abin da zai hana Musulmi zabe
Shugaba Bola Tinubu yana rattaba hannu da mataimakinsa, Kashim Shettima. Hoto: Bayo Onanuga.
Source: Twitter

'Ba a yi wa Kiristoci wariya'

Aliyu ya kuma ce ce-ce-ku-cen da suka biyo bayan tikitin Musulmi–Musulmi a 2023 sun riga sun lafa, yana mai jaddada cewa Kiristoci ba sa fuskantar wariya a ƙarƙashin gwamnatin Shugaba Tinubu.

Ya ce:

“Wannan gwamnati ba ta da wani abin da za a nuna cewa tana fifita Musulmi a kan Kiristoci, don haka ina ganin tikitin Musulmi–Musulmi har yanzu na iya yin tasiri a APC.
“Dangane da Arewar da na sani, Arewa ba za ta ji daɗin tikitin Kirista–Kirista ba, domin idan aka yi haka, za a ware Musulmi gaba ɗaya a Arewa."

Yan APC sun gargadi sauya Shettima a 2027

A wani labarin, Kungiyar APC Youth Parliament North East ta yi karin haske game da jita-jitar da ake yadawa kan maganar sauya Kashim Shettima.

Shugaban kungiyar, Kabiru Garba Kobi daga Bauchi, ya zargi wasu 'yan siyasa da yada rade-radin saboda cimma burinsu.

Kabiru Kobi ya bayyana haka yayin da yake nuna damuwa game da jita-jitar sauya Shettima a ranar Lahadi 25 ga watan Janairun 2026 da muke ciki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.