Siyasar Kano: 'Dan Kwankwaso Ya Zabi Wanda da Zai Bi tsakanin Mahaifinsa da Gwamna Abba

Siyasar Kano: 'Dan Kwankwaso Ya Zabi Wanda da Zai Bi tsakanin Mahaifinsa da Gwamna Abba

  • Alamu sun nuna cewa wasu daga cikin kwamishinonin gwamnatin Kano za su yi murabus idan Gwamna Abba Kabir Yusuf ya koma APC
  • Majiyoyi sun bayyana cewa 'dan Rabiu Kwankwaso, Mustapha ya fara shirye-shiryen ajiye aiki kafin ko bayan Abba Gida-Gida ya bar NNPP
  • Rahoto ya nuna cewa duk da wasu kwamishinoni sun nuna cewa suna tare da Kwankwaso, Abba ya ja tawaga mafi rinjaye a majalisar zartawa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Kwamishinan matasa da wasanni na Kano, Mustapha Kwankwaso na shirin barin mukaminsa gabanin sauyin sheƙar Gwamna Abba Yusuf daga jam’iyyar NNPP zuwa APC.

Mustapha shi ne babban ɗan tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, wanda shi ne jagoran jam'iyyar NNPP kuma tsohon dan takarar shugaban kasa.

Gwamna Abba da dan Kwankwaso.
Gwamna Abba Kabir Yusuf da Kwamishinan Harkokin Matasa da Wasanni, Mustapha Rabiu Kwankwaso Hoto: Abba Kabir Yusuf
Source: Twitter

Premium Times ta ce duk da Mustapha bai mika takardar murabus a hukumance ba, kuma gwamnan bai cire shi daga mukaminsa ba, majiyoyi sun ce zai yi murabus a kafin ko bayan Abba ya bar NNPP.

Kara karanta wannan

"Ni zan masu dariya a karshe," Kwankwaso ya kara tabo batun sauya shekar Gwamna Abba

Dalilin Gwamna Abba na komawa APC

Ko da Gwamna Abba bai bayyana a fili cewa zai fice daga NNPP ba, mataimakansa da ‘yan Majalisar Dokokin Jihar sun tabbatar da shirinsa na komawa APC.

Sun danganta hakan da rikice-rikicen shari’a da ke kara tsananta a cikin NNPP, wanda ya sa suke gudun abin da ya faru da APC a Zamfara, ya faru a Kano.

Shin dan Kwankwaso zai bi Abba zuwa APC?

Majiyoyi sun shaida wa jaridar cewa Mustapha Kwankwaso ya bar ma’aikatarsa tare da kwashe kayansa bayan mahaifinsa, ya nuna rashin amincewa da shirin gwamnan na sauya sheƙa.

Zuwa yau Juma'a, manyan jiga-jigai da masu rike da mukamai da dama sun sake jaddada mubaya'arsu ga Kwankwaso, tare da tabbatar da ba za su bi gwamnan zuwa APC.

Daga cikinsu akwai Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Yusuf Kofar-Mata; Kwamishinan Harkokin Jin-ƙai, Adamu Aliyu; Kwamishinan Tsaron Cikin Gida, Ibrahim Umar da Kwamishinan Albarkatun Ma’adanai, Hamza Kachako.

Kara karanta wannan

Mataimakin shugaban NNPP ya tono wata doka, ya dora Gwamna Abba a saman Kwankwaso

Sauran da aka ruwaito sun sanya hannu a rajistar mubaya'a ga Kwankwaso sun hada da Shugaban Ma’aikatan Kano, Abdullahi Musa; Shugaban Hukumar Tallafin Karatu, Musa Danzaki; da shugaban kasuwar Kwari, Hamisu Dogonnama.

Kwankwaso da Gwamna Abba.
Jagoran NNPP na kasa, Rabiu Kwankwaso tare da Gwamna Abba Kabir Yusuf a wurin taro a Kano Hoto: Saifullahi Hassan
Source: Facebook

Gwamna Abba ya samu rinjaye a NNPP

Amma duk da haka, bayanai sun nuna cewa Gwamma Abba ya samu rinjaye daga cikin yan Majalisar tarayya da na jiha, kamar yadda Leadership ta kawo.

An ruwaito cewa Gwamna Abba Kabir ya samu rinjayen masu goyon baya a cikin masu rike da mukamai, a abin da majiyoyi suka bayyana a matsayin “juyin mulki na cikin gida”.

Dukkan shugabannin kananan hukumomi 44, mataimakansu, da mafi yawan shugabannin mazabu sun bi gwamnan a shirin sauya sheƙa zuwa APC.

Kwankwaso ya soki shirin Gwamna Abba

A wani labarin, kun ji cewa Sanata Rabiu Kwankwaso ya gargadi Gwamna Abba Kabir Yusuf kan shirin komawa jam'iyyar APC, inda ya bayyana hakan da 'cin amana'.

Kwankwaso ya gargaɗi waɗanda ke shirin bin Gwamna Abba zuwa APC cewa lallai akwai sakamako ga duk wanda ya ci amanar tafiyar da ta gina shi.

Tsohon gwamnan na Kano ya bukaci dukkan mambobin NNPP da ke son sauya sheka zuwa APC da su biya diyya ga tafiyar Kwankwasiyya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262