'Yan Majalisa 2 Sun Fice daga Jam'iyyar PDP, Sun Gana da Shugaban Gwamnonin Arewa

'Yan Majalisa 2 Sun Fice daga Jam'iyyar PDP, Sun Gana da Shugaban Gwamnonin Arewa

  • Jam'iyyar APC ta kara mamaye Majalisar dokokin jihar Gombe bayan mambobi biyu sun tabbatar da ficewarsu daga PDP
  • 'Yan Majalisar sun sanar da komawa APC mai mulki domin samun cikakken damar tallafawa manufofin ci gaba na gwamnatin Gombe
  • Gwamna Inuwa Yahaya ya ce wannan sauya sheka ta nuna yadda jama'a suka gamsu tare da aminta da gwamnatinsa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Gombe, Nigeria - Wasu mambobi biyu na Majalisar Dokokin Jihar Gombe daga jam’iyyar adawa ta PDP sun sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki ta APC.

’Yan majalisar da suka sauya sheƙar sun haɗa da Gabriel Galadima Fushison, mai wakiltar Kaltungo ta Yamma, da kuma Malon Nimrod Yari, mai wakiltar Shongom.

Majalisar dokokin jihar Gombe.
'Yan Majalisa a lokacin zamansu a zauren Majalisar dokokin jihar Gombe Hoto: Bello Seyoji
Source: Facebook

'Yan Majalisa 2 sun koma APC a Gombe

Premium Times ta ce sun sanar da ficewarsu a hukumance ne a ranar Laraba, sannan daga bisani suka kai ziyara fadar gwamnatin Gombe inda suka gana da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya.

Kara karanta wannan

Abin boye ya fito: Dalilan da suka sanya Gwamna Abba zai rabu da NNPP zuwa APC

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Gombe, Rt. Hon. bubakar Mohammed Luggerewo, ne ya jagoranci tawagar zuwa fadar gwamnati tare da mataimakinsa, Sadam Bello da sauran shugabannin majalisar.

Dalilan sauya shekar 'yan Majalisa 2

A cewar ’yan majalisar, sun yanke shawarar sauya sheƙa ne sakamakon tsarin shugabanci na haɗin kai, nagarta da kuma kyakkyawan aiki da Gwamna Inuwa Yahaya ke yi tun bayan hawansa mulki.

Sun bayyana cewa ko da suna PDP, hakan bai hana su kyakkyawar mu’amala da bangaren zartarwa ba, inda suka ce mutanen mazabunsu sun amfana da ayyuka da shirye-shiryen gwamnatin jihar.

“Abin da ya sa muka yanke wannan shawara shi ne adalci, nagartaccen shugabanci da kuma jajircewar gwamna wajen tabbatar da ci gaba a faɗin jihar,” in ji ’yan majalisar.

Sun ƙara da cewa shiga APC zai ba su damar tallafa wa manufofin ci gaba na gwamnatin jihar Gombe yadda ya kamata.

Abin da Gwamna Inuwa ya fada masu

Da yake karɓar su cikin APC, Gwamna Inuwa Yahaya, wanda shi ne shugaban gwamnonin Arewa, ya ce sauya shekar ta nuna yadda jama'a suka aminta da gwamnatinsa.

Kara karanta wannan

Tsohon gwamna ya yi amai ya lashe, ya sauya sheka daga PDP zuwa jam'iyyar APC

Ya ba su tabbacin cewa za a ba su cikakken matsayi da kulawa iri ɗaya da sauran mambobin jam’iyyar, kamar yadda jaridar People Gazette Nigeria ta ruwaito.

Gwamnan ya kuma yaba wa shugabancin Majalisar Dokokin jihar bisa kyakkyawar fahimta da haɗin kai da bangaren zartarwa, yana mai cewa hakan ne ya taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Gombe.

Gwamna Inuwa Yahaya.
Gwamna Inuwa Yahaya yana jawabi yayin gabatar da kasafi a majalisar dokokin Gombe Hoto: Muhammad Inuwa Yahaya
Source: Twitter

Ya nuna ƙwarin gwiwar cewa haɗin kai a cikin APC zai kai jam’iyyar ga nasara a zaɓen 2027 a jihar Gombe da ma ƙasa baki ɗaya.

Da wannan sabon ci gaba, jam’iyyar APC yanzu tana da kujeru 23 cikin 24 na Majalisar Dokokin Jihar Gombe, yayin da PDP ta rage da ɗan majalisa guda ɗaya kacal.

Tsohon gwamnan Abia ya koma APC

A wani labarin, kun ji cewa tsohon gwamnan na jihar Abia, Sanata Theodore Orji, ya sanar da dawowa siyasa gadan-gadan, tare da bayyana ficewarsa daga PDP zuwa jam'iyyar APC.

Ana ganin cewa tsohon gwamnan ya na ɗaya daga cikin manyan ginshikan jam’iyyar PDP masu tallafa mata a jihar Abia, kuma komawarsa APC na iya rusa tsarinta gaba daya.

Mai ba tsohon gwamnan shawara kan harkokin yada labarai, Mista Ifeanyi Umere, ya ce maigidansa ya yanke wannan shawara ne bisa ra'ayin kansa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262