PDP Ta Sake Rikicewa: Tsohon Gwamnan Kogi Ya Sauya Sheka zuwa Jam'iyyar APC

PDP Ta Sake Rikicewa: Tsohon Gwamnan Kogi Ya Sauya Sheka zuwa Jam'iyyar APC

  • Tsohon gwamnan jihar Kogi, Idris Wada, ya karɓi katin zama ɗan jam’iyyar APC, wanda hakan ke nufin ya fice daga PDP
  • An bayyana cewa shigar Wada cikin APC ta nuna sabuwar babin siyasa da ke ƙara karfafa tasirin jam’iyyar a jihar Kogi
  • Ana sa ran gwamnan jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, na shirin karbar Wada da magoya bayansa a hukumance cikin APC

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kogi - Idris Ichalla Wada, tsohon gwamnan Kogi, ya sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki a jihar da kasa baki daya, watau APC.

Wada ya karɓi katin zama ɗan jam’iyyar ne a ranar Asabar a gidansa da ke Odu, cikin Karamar Hukumar Dekina ta jihar Kogi.

Tsohon gwamnan Kogi, Idris Wada ya sauya sheka daga PDP zuwa APC
Hoton tsohon gwamnan jihar Kogi, Capt. Idris Wada a wani taron PDP. Hoto: Capt Idris Ichalla Wada
Source: Facebook

Tsohon gwamnan Kogi ya koma APC

Hakan ya tabbatar da cewa tsohon gwamnan ya bar jam’iyyar PDP a hukumance yayin da yake fara sabon shafi na siyasar sa, in ji rahoton TVC News.

Kara karanta wannan

PDP ta rikice: Gwamnoni 2 sun nesanta kansu daga korar Wike, Fayose daga jam'iyya

David Alfred-Dogwo, mai taimaka masa kan yaɗa labarai, ya bayyana cewa Capt. Idris Wada na da kwarin gwiwa game da makomar siyasar sa a APC.

Ya ce kodayake bikin ya kasance gajere ne, muhimmancinsa ya nuna cikakken shigar Wada cikin jam’iyyar tare da karfafa tasirin APC a yankin Kogi ta Kudu.

Ya bayyana cewa manyan shugabannin jam’iyyar APC, magoya baya da masu masa addu’a daga sassa daban-daban na Dekina sun halarci taron.

Sauya shekar Wada ta kara karfin APC

Mai taimaka wa Wada ya ce wannan sauyi zai taimaka wa jam’iyyar wajen kara karfi a Dekina da kuma kara shirye-shiryen APC wajen tunkarar zabubbukan nan gaba a jihar.

Ya kara da cewa hakan zai kuma karfafa goyon bayan jam’iyyar ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben shekarar 2027.

Wada ya rike kujerar gwamnan Kogi daga Janairu 2012 zuwa Janairu 2016 a karkashin PDP, amma ya gaza lashe zaben tazarce.

Kara karanta wannan

Ta faru ta kare: PDP ta fatattaki Wike, tsohon gwamna da wasu da ke kawo mata cikas

INEC ta ayyana zaben Kogi da aka gudanar a ranar 21 ga Nuwamba 2015 a matsayin wanda bai kammalu ba, wanda hakan ya kai ga sake shirya sabon zabe a ranar 5 ga Disamba 2015.

Dan takarar APC na wancan lokaci, Abubakar Audu, ya rasu a ranar 22 ga Nuwamba — kwana guda bayan gudanar da zaben farko.

A karshe, bayan gudanar sabon zabe, hukumar INEC ta bayyana dan takarar maye gurbin APC, Yahaya Bello, a matsayin wanda ya ci zaben.

Gwamna Usman Ododo ne zai tarbi Idris Wada zuwa APC a hukumance.
Hoton gwamnan jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo. Hoto: @OfficialOAU
Source: Twitter

Gwamna Ododo zai tarbi Wada da magoya bayansa

Gwamnan jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, na shirin karbar Wada da magoya bayansa a hukumance cikin jam’iyyar APC, in ji rahoton The Authority.

A wata sanarwa da mai ba shi shawara kan labarai, Ismaila Isah, ya fitar, an ce za a yi taron tarbar sauya shekar ne a ranar Litinin a dandalin Muhammadu Buhari Square da ke Lokoja.

Taron zai samu halartar manyan shugabannin jam’iyyar a matakin jiha da kasa, inda za a tabbatar da shigowar Wada cikin jam’iyyar.

Abia: Tsohon gwamna ya koma APC

A wani labarin, mun ruwaito cewa, tsohon gwamnan Abia, Sanata Theodore Orji ya mika takardar murabus ga shugaban jam'iyyar PDP a jiharsa.

Kara karanta wannan

PDP ta yi watsi da Wike da mutanensa, ta ce 'babu fashi' kan taronta na Oyo

Sanata Orji wanda ya mulki jihar Abia na tsawon shekaru takwas, ya ce ya yanke shawarar fita daga PDP ne bayan tattaunawa da abokan siyasarsa.

Wannan na zuwa ne a ranar da jam'iyyar PDP karkashin jagorancin Ambasada Umar Damagum ta fara babban taro na kasa a Ibadan, jihar Oyo.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com