Charles Soludo da 'Yan Takara 3 da za Su Gwabza a Zaben Gwamnan Anambra

Charles Soludo da 'Yan Takara 3 da za Su Gwabza a Zaben Gwamnan Anambra

A ranar Asabar, Gwamna Charles Soludo na jihar Anambra zai fuskanci Nicholas Ukachukwu na jam’iyyar APC da wasu ‘yan takara 14 da ke neman kujerarsa a zaben gwamnan jihar Anambra.

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Anambra –Daga cikin ‘yan takara 16 da za su fafata a zaben da za a gudanar a ranar 8 ga Nuwamba, 2025, mutum hudu ne kacal ake ganin za su iya kai labari a zaben.

'Yan takara 4 sun dauki hankali a zaben Anambra mai zuwa
Charles Soludo, Nicholas Ukachukwu, Ezenwafor Jude Hoto: Chukwuma Charles Soludo/Nicholas Ukachukwu Media Office/Ezenwafor Jude Digar
Source: Facebook

Premium Times ta wallafa cewa waɗannan manyan ‘yan takarar su ne: gwamna mai ci, Charles Soludo na APGA; fitaccen ɗan kasuwa, Nicholas Ukachukwu na APC.

Sai kuma tsohon babban darektan Hukumar Ruwa ta Ƙasa (NIWA), George Moghalu na LP da kuma ɗan kasuwa kuma masanin tattalin arziki, John Chuma-Nwosu na ADC.

Kara karanta wannan

Abubuwan da ba ku sani ba game da Zohran Mamdani, sabon magajin garin New York

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. Charles Chukwuma Soludo

This Day ta ruwaito cewa Charles Chukwuma Soludo shi ne gwamna mai ci na jihar Anambra, wanda hakan ke ba shi wani babban rinjaye a kan sauran ‘yan takara.

Soludo na takara a ƙarƙashin APGA, jam’iyyar da ta riƙe mulki a jihar sama da shekaru 20. Yana takara tare da Dr. Onyeka Ibezim, ƙanin Bishof na cocin Anglican, Awka Diocese.

Charles Soludo na son ya cigaba da mulkin Anambra
Gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo Hoto: ccSoludo
Source: Facebook

Idan aka yi la’akari da tsarin addini a siyasar Anambra, Soludo da mataimakinsa suna da damar nasara saboda Soludo ɗan cocin Katolika ne — addinin da yawanci ke samar da gwamna a jihar.

Ana ganin Soludo da jam’iyyarsa APGA suna da babban damar lashe zaben, musamman ganin yadda jama’a da dama ke ganin ya yi aiki mai kyau a zangonsa na farko.

2. Nicholas Ukachukwu

Nicholas Ukachukwu ɗan kasuwa ne kuma gogaggen mai narka kudi a harkar kasuwancin gidaje, kuma shi ne ɗan takarar jam’iyyar APC.

Kara karanta wannan

Sojoji sun gwabza faɗa da ƴan ta'addan Boko Haram a Borno, an samu asarar rayuka

Ana ganin yana da kyakkyawar damar nasara saboda jam’iyyarsa ce ke mulki a ƙasar nan.

Nicholas Ukachukwu na neman takarar gwamna a Anambra
Hoton Nicholas Ukachukwu, 'dan takarar gwamna a aAnambra Charles@OfficialAPCNg
Source: Facebook

Yana takara a tikiti guda tare da Sanata Uche Ekwunife, wadda ta shahara a siyasar ƙasa da ta taba neman kujerar gwamna a baya.

Shahararta na iya ƙara farin jinin Ukachukwu a wannan zabe. Sai dai ƙarancin karatun dan takarar ya zamar masa matsala a yayin kamfen.

3. George Moghalu

Cif George Moghalu, tsohon babban darektan Hukumar Ruwa ta Ƙasa (NIWA), shi ne ɗan takarar jam’iyyar LP a zaɓen jihar.

Ɗan asalin garin Nnewi ne, kuma ya yi ƙoƙari sosai wajen samun tikitin jam’iyyarsa saboda rikicin shugabanci da ke damun jam’iyyar a matakin ƙasa.

George Mogahalu na neman takara a inuwar LP
Hoton Goerge Moghalu, dan takarar gwamnan Anambra a LP Hoto: @OKEKEOLIVER2
Source: Twitter

Moghalu gogaggen ɗan takarar gwamna ne tun zamanin jam’iyyar APP. Yana da goyon bayan tsohon gwamnan jihar, Peter Obi, amma hakan kadai bai wadatar masa ba don lashe zabe.

Shi ɗan cocin Anglican ne, kuma ana ganin kamfen ɗinsa ya fi karkata wajen sukar gwamnatin Soludo da nuna kura-kuransa, fiye da bayyana shirin kansa ga jihar.

Kara karanta wannan

Jira ya kare: Hukumar NSIEC ta fitar da sakamakon zaben kananan hukumomin Neja

4. Jude Ezenwafor

Ɗan takarar jam’iyyar PDP a zaben gwamnan Anambra na ranar 8 ga Nuwamba, 2025, shi ne Cif Jude Ezenwafor.

Ya yi alkawarin magance matsalolin tsaro, ilimi, hanyoyi da harkar kasuwanci idan aka zaɓe shi.

Ya kuma ce zai rage nauyin haraji da aka dora wa ‘yan jihar domin ƙarfafa harkar kasuwanci da bunƙasa tattalin arziki.

Jude Ezenwafor, shi ne wanda ke neman gwamnan Anambra a inuwar PDP
Hoton Jude Ezenwafor, dan takarar gwamnan PDP a Anambra Hoto: Ezenwafor Jude Digar
Source: Facebook

Daily Post ta ruwaito cewa a watan Yuli na shekarar 2025 ne aka samu rahoton cewa wasu 'yan sun tare dan takarar tare da bude masa wuta a hayarsa ta komawa gida a babban birnin tarayaa, Abuja.

Makusantansa da wasu daga cikin manyan PDP sun bayyana damuwa cewa wannan lamarin na iya shafar tsarin yakin neman zaben jam’iyyar, musamman idan raunin da Ezenwafor ya tsananta.

Wata majiya ta bayyana cewa:

“Za mu duba yadda lafiyarsa take kafin mu yanke shawara kan yadda za mu ci gaba da kamfen. Muna fatan zai samu sauƙi cikin gaggawa.”

Kara karanta wannan

APC ta samu rinjaye, ta kulle damar tsige Shugaban ƙasa a majalisa

Sai dai Jude Ezenwafor ya murmure, kuma shi da jam'iyyarsa ta PDP sun shirya shiga domin a fafata a zaben ranar Asabar mai zuwa.

An jibge jami'an tsaro a Anambra

A baya, mun wallafa cewa rundunar 'yan sanda ta tura jami’an tsaro sama da 60 000 daga hukumomin tsaro daban-daban domin tabbatar da tsaro a lokacin zaben gwamnan Anambra.

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Abayomi Shogunle, ya bayyana cewa an kafa cibiyar ta musamman wacce za ta raba bayanai tsakanin hukumomin tsaro cikin gaggawa domin inganta aiki.

Shogunle ya ce an shirya rundunoni na tsaro a kowace daga cikin rumfunan zabe guda 5,720 a aka samar a fadin jihar domin daukar matakan kare masu kada kuri'a daga duk wani hari ko rikici.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng