Jerin Gwamnonin Adawa a Najeriya da Suka Bar Jam’iyyunsu zuwa APC a 2025
Jam'iyyyar APC mai mulki a Najeriya na ci gaba da karbar gwamnonin jam'iyyun adawa wadanda suke sauya sheka zuwa cikinta saboda wasu dalilai.
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - A cikin shekarar 2025 kadai, akalla manyan gwamnoni uku ne suka bar jam'iyyarsu ta PDP mai adawa a kasar zuwa APC domin ci gaba da ayyukan alheri ga jihohinsu.

Source: Facebook
Rahoton Punch ya ce har yanzu ana hasashen wasu gwamnoni daga jam'iyyar PDP za su shiga APC kafin zaben shekarar 2027 da ake tunkara.
Majiyoyi suka ce hasashen cewa wasu gwamnonin adawa na shirin komawa APC ya yi karfi sosai duk da cewa sun karyata hakan a lokuta da dama.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Daga cikin gwamnonin da aka yi hasashen za su koma APC akwai na Taraba, Agbu Kefas da na Osun, Ademola Adeleke da kuma na jihar Abia, Alex Otti wanda daga baya suka karyata hakan.

Kara karanta wannan
Gwamna ya bi sahun Peter Mbah ya koma jam'iyyar APC mai mulki? Gaskiya ta bayyana
Gwamnoni da suka koma APC a 2025
Legit Hausa ta yi duba kan gwamnonin Najeriya uku da suka bar jam'iyyarsu ta PDP zuwa APC mai mulkin Najeriya da kuma daya da ya yi murabus ba tare da shiga wata jam'iyya ba.
1. Gwamna Sheriff Oborevwori - Delta
Bayan yada jita-jitar sauya sheka da aka yi ta yadawa, gwamnan jihar Delta ya watsar da PDP duk da karyata cewa zai koma APC da ake fada zai yi.
Gwamna Sheriff Oborevwori, ya sauya sheƙa daga jam’iyyar PDP zuwa APC a wani babban sauyin siyasa da ya dauki hankula.
Ya sanar da haka ne a wata ganawar sirri da aka gudanar a gidan gwamnati da ke Asaba, inda manyan shugabannin APC suka karɓe shi hannu biyu biyu.
Sauyin jam’iyyar ya zo daidai lokacin da ake fuskantar sauye-sauye a siyasar jihar Delta, tare da shirye-shiryen murza gashin baki domin zaɓen 2027.

Source: Facebook
2. Gwamna Umo Eno - Akwa Ibom
Gwamnan da ya biyo bayan na jihar Delta, shi ne gwamnan Akwa Ibom wanda ya yi ta maza ya bar PDP domin tarewa da jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya.

Kara karanta wannan
Shettima zai taso daga Abuja domin karbar wasu manyan 'yan siyasar Arewa zuwa APC
Bayan jita-jitar cewa ba zai bar PDP ba, Gwamna Umo Eno na jihar Akwa Ibom ya sauya sheka daga jam'iyyar zuwa APC mai mulkin Najeriya a ranar Juma'a 6 ga watan Yunin 2025.
Gwamna Eno ya sanar da haka ne a wani taro na musamnan da aka shirya a fadar gwamnatinsa da ke Uyo, babban birnin jihar Akwa Ibom.
Gwamnonin APC ƙarƙashin jagoranci Gwamna Hope Uzodinma na jihar Imo ne suka tarbi Fasto Umo Eno a hukumance, cewar rahoton Channels TV.

Source: Facebook
3. Gwamna Peter Mbah - Enugu
A ranar 14 ga watan Oktobar 2025, jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya ta yi babban rashi na daya daga cikin gwamnoninta daga Kudancin Najeriya.
Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah ya sanar da komawarsa jam’iyyar APC daga PDP a taron manema labarai da ya gudana a Enugu.
Peter Mbah ya ce matakin ya biyo bayan dogon tunani ne domin neman hadin kai da gwamnatin tarayya wajen bunkasa jihar.
Gwamnan ya bayyana cewa wannan mataki zai ba Enugu da yankin Kudu maso Gabas damar samun karin tasiri a gwamnatin Bola Tinubu.

Source: Facebook
Gwamna Diri ya yi murabus a PDP
A ranar 15 ga watan Oktobar 2025 ne Gwamna Douye Diri ya tabbatar yin murabus tare da wasu mukarrabansa daga PDP, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.
Kwana daya bayan sauya shekar gwamnan Enugu daga PDP, takwaransa daga jam'iyyar hamayyar ya yi murabus daga cikinta.
Gwamna Douye Diri na jihar Bayelsa ya sanar da barinsa jam’iyyar PDP a wani taro da aka gudanar a gidan gwamnati a Yenagoa.
Sai dai har yanzu Gwamna Diri bai bayyana jam'iyyar da zai koma ba bayan murabus din wanda ya fara jawo maganganu duk da cewa masana na cewa APC zai koma a karshe.

Source: Twitter
'Gwamnoni 4 za su koma APC' - Fasto
A baya, kun ji cewa babban malamin addinin Kirista, Elijah Ayodele ya yi hasashe game da wasu gwamnonin adawa da ya ce za su iya komawa APC.
Malamin ya gargadi ga Bola Tinubu cewa wasu gwamnonin adawa za su koma APC amma ba duka ne ke son taimaka masa.
Limamin ya ce wasu daga cikinsu za su shiga jam’iyyar ne kawai don su sami albarkar shugaban ƙasa da kuma neman mukamai.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Asali: Legit.ng

