ADC Ta Taso APC a gaba, Ta Fallasa Makircin da Ake Shiryawa 'Yan Adawa
- Jam'iyyar ADC ta nuna rashin gamsuwarta da yadda hukumar yaki da cin hanci ta EFCC ta ke gudanar da ayyukanta
- ADC ta yi zargin cewa jam'iyyar APC ta mayar da hukumar EFCC karen farautar ta domin yi wa 'yan adawa barazana
- Jam'iyyar ADC ta nuna cewa hakan ba karamar illa ba ce, yana zubar da kimar hukumar EFCC a idon 'yan Najeriya
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Jam’iyyar ADC ta zargi APC mai mulki da amfani da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa (EFCC) a matsayin makami don tsoratar da ‘yan siyasar adawa.
Jam'iyyar ADC ta yi gargadin cewa irin wannan lamari yana lalata amincewar jama’a ga hukumar da kuma raunana yaki da cin hanci a Najeriya.

Asali: Facebook
Hakan ne kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar ADC na kasa, Malam Bolaji Abdullahi, ya sanya a shafin X a ranar Litinin, 11 ga watan Agustan 2025.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Wane zargi jam'iyyar ADC ta yi wa APC?
Jam'iyyar ADC ta yi ikirarin cewa a matakan baya-bayan nan na EFCC, ciki har da dawo da ci gaba da tsofaffin shari’o’i da kuma gayyatar mambobin adawa, akwai siyasa a ciki.
"An kafa EFCC ne domin ta kasance mai kare amanar al’ummar Najeriya ba tare da tsoro ba, tana aiwatar da doka daidai ga kowa, aboki ko makiyi, jam’iyya mai mulki ko ta adawa. Yanzu, ba haka abubuwan suke ba."
"Yanzu hukumar tana aiki kamar wani sashen APC, ana amfani da ita don yaƙar masu sukar gwamnati da ‘yan adawa, ta haka tana cimma abin da gwamnati ba za ta iya cimmawa ta hanyar muhawara a bainar jama’a ba."
- Bolaji Abdullahi
Jam’iyyar ta zargi EFCC da son kai wajen gurfanarwa, tana kawo misalan yadda ake daina bincike kan 'yan siyasar APC yayin da ake ci gaba da farfado da zarge-zargen da ake yi wa ‘yan adawa.
“Tun da wani tsohon gwamna ya koma APC tare da dukkan tsarin siyasar jiharsa, binciken EFCC kan gwamnatinsa ya bace daga idon jama’a. Ba a taba yin tambaya ba. Ba wata takarda da aka fitar. Ba wani sabon bayani."
"A Najeriya ta yau, alamar laifi ko rashin laifi ya dogare ne da jam’iyyar da mutum ke ciki, ba hujja ba."
- Bolaji Abdullahi

Asali: Facebook
ADC ta nuna kuskuren bata ayyukan EFCC
A cewar ADC, irin wannan nuna bambanci yana lalata kimar EFCC da kuma yaki da cin hanci baki daya.
Ta yi gargadin cewa kallon EFCC a matsayin hukumar bi ta kulli kan siyasa yana rage amincewar jama’a kuma yana haifar da rashin amanna kan ayyukanta.
“EFCC ba mallakar APC ba ce. Ta al’ummar Najeriya ce. Da kudaden harajin jama’a ake daukar nauyinta, ba na jam’iyya mai mulki ba."
- Bolaji Abdullahi
Sakaten gwamnatin Buhari ya musanta shiga ADC
A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon sakataren gwamnatin tarayya a zamanin mulkin marigayi, Muhammadu Buhari, Boss Mustapha, ya nesanta kansa da batun komawa jam'iyyar ADC.
Tsohon sakataren gwamnatin tarayyar ya musanta cewa ya sauya sheka daga jam'iyyar APC zuwa ADC mai adawa.
Boss Mustapha ya bayyana cewa zai ci gaba da zama a APC wadda ya ba gudunmawa wajen kafuwarta.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng