'Rasuwar Buhari ba Za Ta Kawo Cikas ga Tazarcen Tinubu ba a 2027,' Sanata Adeyeye

'Rasuwar Buhari ba Za Ta Kawo Cikas ga Tazarcen Tinubu ba a 2027,' Sanata Adeyeye

  • Akwai wasu masu sharhi da ke tunanin cewa rasuwar marigayi Muhammadu Buhari za ta iya kawo cikas ga tazarcen Bola Tinubu a 2027
  • Sanata Dayo Adeyeye ya bayyana cewa wannan hasashen ko kadan ba daidai ba ne domin Tinubu bai dogara da tasirin Buhari ba
  • Ya nuna cewa ko a zaben shekarar 2023, ba tasirin Buhari ba ne ya sanya ya samu nasarar zama shugaban kasa a jam'iyyar APC

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Legas - Tsohon sanata a jihar Osun, Dayo Adeyeye, ya yi magana kan alakar rasuwar tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da tazarcen Bola Ahmed Tinubu.

Dayo Adeyeye ya ce rasuwar marigayi Buhari ba za ta kawo cikas ba ga Shugaba Bola Tinubu a zaben shekarar 2027.

Shugaban kungiyar SWAGA ya yi magana kan tazarcen Tinubu
Dayo Adeyeye ya yi magana kan tazarcen Shugaba Tinubu Hoto: @DOlusegun, @MBuhari
Source: Twitter

Adeyeye wanda tsohon karamin ministan ayyuka ne, ya bayyana hakan ne yayin da yake magana da ’yan jarida a ranar Asabar a Legas, cewar rahoton jaridar The Punch.

Kara karanta wannan

Najeriya ta yi babban rashi, tsohon ministan Buhari, Audu Ogbeh ya rasu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya yi wannan bayani ne a matsayin martani kan kalaman da wasu ke yi na cewa tasirin Buhari ya taimaka wajen nasarar Tinubu a zaben 2023, kuma rasuwarsa za ta iya kawo cikas ga tazarcensa a 2027.

Rasuwar Buhari ba za ta rage tasirin Tinubu ba

A cewar Adeyeye, tattaunawar da ake yi cewa rasuwar Buhari za ta rage kuri’un Tinubu a Arewa tana kan kuskuren fahimta.

Tsohon ministan, wanda kuma shi ne shugaban ƙungiyar South West Agenda for Asiwaju (SWAGA) ya ce Tinubu bai amfani da suna ko farin jinin Buhari a Arewa ba wajen samun nasara a 2023, rahoton Vanguard ya tabbatar.

Ya bayyana cewa shugaban kasa na ci gaba da samun goyon baya a faɗin ƙasar nan sakamakon ƙoƙarinsa da jajircewarsa.

"Ba daidai ba ne. A gaskiya, Tinubu zai samu ƙarin kuri’u a Arewa da sauran wurare a 2027 fiye da kowane lokaci a tarihin kasar nan."

Kara karanta wannan

2027: An ji ra'ayin Jonathan kan fafatawa da Shugaba Tinubu

- Dayo Adeyeye

Dayo Adeyeye ya kuma bayyana cewa ba gaskiya ba ne jita-jitar da ake yadawa cewa bangaren CPC da ke cikin APC ya janye goyon bayansa ga Tinubu.

Ya ce fiye da kashi 90% cikin 100% na mambobin bangaren CPC har yanzu suna goyon bayan shugaban kasan da tazarcensa.

Ana rade-radin Shugaba Bola Tinubu zai nemi tazarce
Shugaba Tinubu bai fito ya ce zai yi tazarce ba Hoto: @DOlusegun
Source: Facebook

Tinubu na da goyon bayan Kudu maso Yamma

Game da jita-jitar cewa gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, na shirin yin takara da Tinubu a 2027, Adeyeye ya ce ko da hakan gaskiya ne, ba zai kawo matsala ga tasirin Tinubu ba a yankin Kudu maso Yamma.

Ya ce, ko da yake Gwamna Makinde ya cancanci yin takarar shugaban kasa, wannan buri nasa ba zai zama barazana ga Tinubu ba.

"A’a, ba barazana ba ce kwata-kwata. Babu tasiri. Mutane ba wawaye ba ne. Seyi Makinde mutum ne nagari, gwamna mai kyau kuma mai cancantar yin takarar shugabanci, amma ba zai kwace ko kuri’a ɗaya daga hannun Tinubu a 2027 ba."

Kara karanta wannan

APC ta yi watsi da kalaman El Rufai, ta fadi dalilin da zai sa Tinubu yin tazarce a 2027

- Dayo Adeyeye

Tsohon ministan Buhari ya rasu

A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon minista a gwamnatin marigayi Muhammadu Buhari, ya yi bankwana da duniya.

Audu Ogbeh wanda ya taba zama shugaban jam'iyyar PDP na kasa, ya rasu ne a ranar Asabar, 9 ga watan Agustan 2025.

Iyalan tsohon ministan na noma sun bayyana cewa ya yi bankwana da duniya ne cikin lumana bayan ya hidimtawa Najeriya a matakai daban-daban.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng