'Yadda Aka Tono Wasiƙar Murabus Ɗin Atiku babu Izini Ana Alhinin Rasuwar Buhari'

'Yadda Aka Tono Wasiƙar Murabus Ɗin Atiku babu Izini Ana Alhinin Rasuwar Buhari'

  • Hadimin Atiku Abubakar ya ce an tono wasikar murabus din mai gidansa daga jam’iyyar PDP ba tare da izini ba, aka yada a bainar jama’a
  • Paul Ibe ya bayyana cewa wasu 'yan PDP da ke hada kai da APC ne suka fitar da wasikar domin su raunana Atiku, musamman a lokacin juyayi
  • A cewarsa, kamata ya yi a maida hankalikan mutuwar Buhari, ba wai rikicin siyasa ba, yana mai sukar ministan sufurin jiragen sama

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

FCT, Abuja - Mai ba da shawara ga Atiku Abubakar kan harkokin yada labarai ya yi magana bayan murabus din mai gidansa.

Paul Ibe ya bayyana cewa an tono wasikar murabus din Atiku Abubakar daga PDP ba tare da izini ba inda ya soki wasu yan APC da PDP kan fitar wasikar.

Kara karanta wannan

"An karya doka," Abin da Atiku ya yi ana jimamin rasuwar Buhari ya harzuƙa Ministan Tinubu

An gano yadda aka bankado wasikar murabus din Atiku
An zargi wasu yan PDP da fitar da takardar murabus din Atiku. Hoto: Atiku Abubakar.
Source: Twitter

Yayin wata hira da Arise News a daren Laraba 16 ga watan Yulin 2025, Ibe ya yi bayani kan cece-kuce da ke tattare da lokacin da wasikar ta bayyana a bainar jama’a.

Musabbabin murabus din Atiku daga PDP

Atiku ya aike da takardar murabus dinsa daga PDP a ranar 14 ga Yuli, 2025, zuwa shugaban jam’iyya na unguwarsu da ke Jihar Adamawa.

Daga baya, hadiminsa a kafafen sada zumunta ya wallafa wasikar, inda Atiku ya ce akwai “bambance-bambancen da ba za a sasanta su ba.”

Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar PDP ta kau daga manufofin da aka kafa ta akansu, abin da ya tilasta masa daukar wannan mataki.

Yadda wasikar murabus din Atiku ta bayyana
An zargi wasu a APC, PDP da tono takardar murabus din Atiku. Hoto: Atiku Abubakar.
Source: Twitter

Murabus din Atiku: An zargin 'yan APC, PDP

Paul ya ce wasu da ke kokarin hana Atiku Abubakar ci gaba da siyasa, ciki har da ’yan PDP da abokansu a APC ne suka fitar da wasikar murabus din.

Kara karanta wannan

2027: A ƙarshe, Atiku Abubakar ya yi murabus daga jam'iyyar PDP mai adawa

Ibe ya kira wadanda suka fitar da wasikar da “baragurbin ’yan PDP da ke aiki tare da ’yan APC,” ya ce ya kamata a girmama Buhari yanzu, cewar The Nation.

Ibe ya ce:

"Wadanda ke cewa sun san dalilin murabus dinsa, shin su annabawa ne? Ya kamata mu tattauna wani batu ba wannan ba.
"Mun samu kanmu a wannan halin ne saboda wasu da ba su fatan alheri ga Atiku Abubakar suka tono wasikarsa. Eh, an tono ta.
"Abin takaici ne cewa ministan sufurin jiragen sama, wanda ya kamata ya fi mayar da hankali kan ayyukan jiragen sama, ya tsoma baki a lamarin."

Makinde ya magantu bayan murabus din Atiku

Kun ji cewa bayan Atiku Abubakar ya ɗauki matakin ficewa daga jam'iyyar PDP, hakan ya fara jawo hankulan gwamnoni a Najeriya wanda suka fara magana kan lamarin.

Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo shi ya fara magana inda ya bayyana cewa tafiyar Atiku ba za ta yi wa PDP illa ba, face ta ba ta damar warware wasu matsalolinta.

Makinde ya ce kowane ɗan siyasa na da ƴancin shiga PDP ko ya fita, amma duk wanda zai zama matsala gara ya yi tafiyarsa inda ya ce fitar Atiku babu abin da zai mata.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.