2027: Shekarau, Amaechi da Jerin Tsofaffin Gwamnoni da Ministoci da Suka Shiga ADC

2027: Shekarau, Amaechi da Jerin Tsofaffin Gwamnoni da Ministoci da Suka Shiga ADC

  • Manyan jiga-jigan siyasa a Najeriya sun sauya sheka zuwa jam’iyyar ADC, inda suka kafa hadakar adawa mai karfi gabanin zaben 2027
  • ADC na ci gaba da karbuwa a Najeriya yayin da rahotanni ke nuna cewa wasu gwamnoni da ministoci suna dab da sauya sheka zuwa jam'iyyar
  • A wannan rahoton mun jero tsofaffin ministoci da tsofaffin gwamnoni da suka shiga ADC domin kalubalantar AP da PDP a 2027

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja – Ana ci gaba da samun gagarumin sauyin fasalin siyasa a Najeriya, yayin da manyan jiga-jigan siyasa suka sauya sheka zuwa jam’iyyar ADC.

Wannan alama ce karara cewa ADC ta dauki mikatin zama wata babbar rundunar 'yan adawa da ba a taba gani ba gabanin babban zaben 2027.

Zaɓen 2027: Jerin tsofaffin gwamnoni da ministoci da suka shiga kawancen jam’iyyar ADC. Hoto: ADC/X
Atiku, Amaechi, Obi, El-Rufai, Aregbesola da manyan 'yan adawa sun kaddamar da jam'iyyar ADC. Hoto: ADC/X
Source: Facebook

Tsofaffin ministocin Buhari sun ce sai ADC

A sahun gaba cikin waɗanda suka sauya sheka akwai tsofaffin ministocin gwamnatin Muhammadu Buhari da suka hada da:

Kara karanta wannan

An yi gagarumin taron ADC a Gombe, 'yan APC da PDP sun shiga hadaka

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

  1. Rotimi Amaechi (Tsohon ministan sufuri)
  2. Abubakar Malami (Tsohon ministan shari'a)
  3. Rauf Aregbesola (Tsohon ministan harkokin cikin gida)
  4. Hadi Sirika (Tsohon ministan sufurin jiragen sama)

Wadannan jiga-jigan, wadanda suka kasance ginshikai a mulkin APC, sun bayyana kin amincewarsu da tafiyar jam’iyyar, suna mai cewa lokaci ya yi da za a kafa sabuwar jam’iyya mai gaskiya da ma’ana ga al’umma.

Masana na ganin sauya shekar na wadannan tsofaffin ministoci a matsayin babban sauyi da ke iya sauya taswirar siyasar Najeriya, inda suka taru a inuwa daya domin kalubalantar APC da ma PDP.

David Mark da haduwar tsofaffin gwamnoni a ADC

Tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata David Mark, wanda ya shafe shekaru a jam’iyyar PDP, ya zama shugaban riko na ADC tun a watan Mayu.

A gefe guda kuma, Rauf Aregbesola, tsohon gwamnan Osun shi ne ke rike da mukamin sakataren ADC na kasa, wanda ke nuna cewa jam’iyyar na kokarin hada kwararru don tunkarar 2027.

Kara karanta wannan

ADC ta shiga Borno da karfinta, tana wawashe yan PDP da APC gabanin 2027

Daga cikin wadanda suka kafa kawancen 'yan adawa akwai tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, wanda yake aiki kafada-da-kafa da Atiku Abubakar a ADC.

John Odigie-Oyegun, tsohon gwamnan Edo da kuma shugaban farko na APC, shi ma ya sauya sheka zuwa ADC – lamarin da ke jawo hankula, inji rahoton Vanguard.

A matsayin daya daga cikin waɗanda suka gina APC tun 2015, ficewarsa daga jam’iyyar na nuna rashin gamsuwa da yadda lamura ke tafiya yanzu.

A matakin jihohi, Ahmed Mahmud Gumel, tsohon mataimakin gwamnan jihar Jigawa, ya zama kwamishinan ADC na jiha.

Duk da cewa Peter Obi, tsohon dan takarar shugaban kasa na 2023 kuma tsohon gwamnan Anambra, bai yi rajista da ADC a hukumance ba, amma ya halarci taron kaddamar da jam'iyyar.

Hakazalika, mun ruwaito cewa tsohon gwamnan Kano, Mallam Ibrahim Shekarau da kungiyarsa sun shiga hadakar kawancensu Atiku da kuma jam'iyyar ADC.

Akwai kuma rahoton da ya nuna cewa tsofaffin gwamnonin jihohin Benue, Cross River da Jigawa – Gabriel Suswam, Liyel Imoke, da Sule Lamido suna cikin tattaunawa don shiga hadakar ADC, ko su goyi bayanta a bayan fage.

Kara karanta wannan

Yadda jagororin APC suka ki tarbar Kashim Shettima a Kano bayan Ganduje ya yi murabus

Tsofaffin gwamnoni da tsofaffin ministoci sun shiga hadakar kawancensu Atiku Abubakar
Atiku Abubakar ya gana da tsofaffin gwamnoni da jiga-jigan PDP kan shiga jam'iyyar ADC. Hoto: @atiku
Source: Facebook

Tasirin ADC a siyasar Najeriya gabanin 2027

A cewar majiyoyin daga ADC, gwamnonin jihohi biyar da tsoffin ministoci 14 suna a matakin karshe na shirin sauya sheka zuwa jam’iyyar.

Har yanzu dai ana ci gaba da boye sunayensu, domin dalilan dabarun siyasa yayin da ake tattaunawa da su a sirrance.

Wannan sabon ci gaba na zuwa ne a daidai lokacin da talauci, rashin tsaro da gajiya da mulkin APC ke kara tasirin a tsakanin 'yan Najeriya.

Ko da yake akwai shakku a wasu sassa game da dorewar wannan hadaka, amma kowa ya amince cewa ADC na samun karbuwa a halin yanzu.

Yanzu haka, zaɓen 2027 na kara daukar zafi, inda hadakar ADC ke karɓar manyan jiga-jigan siyasa, kuma idan har aka ci gaba da haka, jam’iyyar na iya zama wadda za ta sauya alkiblar siyasar Najeriya gaba ɗaya.

'Atiku ta zama jam'iyyar doke APC a 2027'

Tun da fari, mun ruwaito cewa, kawancen masu adawa da gwamnatin APC ƙarƙashin jagorancin Atiku Abubakar sun amince da ADC a matsayin jam'iyyar hadaka gabanin zaɓen 2027.

Kara karanta wannan

Rahoto: Muhimman ayyukan alheri 7 da za a tuna marigayi Aminu Dantata da su

An naɗa tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark matsayin shugaban ADC na ƙasa, yayin da Rauf Aregbesola ya zama sakatare, sai kuma Bolaji Abdullahi a matsayin kakakin jam’iyyar.

Manyan jiga-jigan siyasa irin su Atiku Abubakar, Peter Obi da Nasir El-Rufai sun bayyana kwarin guiwar cewa ADC za ta iya doke APC da Shugaba Bola Tinubu a babban zaɓen 2027.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com