"Gara Mu Faɗi Gaskiya," Ministan Jirage Ya Faɗi Gwamnan da Tinubu da APC Ke Tsoronsa gabanin 2027

"Gara Mu Faɗi Gaskiya," Ministan Jirage Ya Faɗi Gwamnan da Tinubu da APC Ke Tsoronsa gabanin 2027

  • Festus Keyamo ya fito ya nuna cewa Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu tana tsoron Gwamna Peter Mbah na jihar Enugu saboda nasarorin da yake samu
  • Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo SAN ne ya bayyana hakan yau Litinin, ya ce APC ta rasa hanyar da za ta bi ta kwace jihar Enugu
  • Keyamo ya ce buƙaci Gwamna Mbah ya kula da kamfanin sufurin jiragen sama na Enugu Air, wanda aka kaddamar yau Litinin, 7 ga watan Yuli

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Enugu - Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, a ranar Litinin ya yaba da irin nasarorin da Gwamnan Jihar Enugu, Dr Peter Mbah, ya samu.

Keyamo ya ce Gwamna Mbah yana daya daga cikin gwamnonin da suka fi kowa kyakkyawan aiki a Najeriya, duk da kasancewarsa dan jam’iyyar adawa ta PDP.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Najeriya ta yi magana kan ƙera makamin nukiliya bayan yaƙin Iran da Isra'ila

Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo.
Gwamnatin Tinibu ta ce tana tsoron haɗuwa da Gwamna Peter Mbah a akwatun zaɓe Hoto: @fkeyamo
Source: Facebook

Ministan ya bayyana haka ne yayin ƙaddamar da sabon kamfanin jirgin sama na Enugu Air a birnin Enugu yau Litinin, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wane gwamna ne Tinubu, APC ke tsoro?

Keyamo ya jinjina tare da yabon salon shugabanci da nasarorin da Gwamna Mbah ke samu tun da ya hau kan mulki a 2023 zuwa yau.

“Bari na maimaita abin da shugaban ƙasa ya ce kwanakin baya yayin kaddamar da wani aiki. Dr Peter Mbah, kai ɗan PDP ne, amma muna jin tsoronka.
"Hanyar da kake bi tana tayar mana da hankali, ba mu san yadda za mu tsara dabarar da za mu kayar da kai a zaɓe ba, amma muna kan shiri.
"Duk da bambancin jam’iyya, bai kamata mu ji tsoron faɗin gaskiya ba. Kana da burin ci gaba, ka yi abin a zo a gani a Jihar Enugu, kuma kana daga cikin gwamnoni mafi aiki.”

Kara karanta wannan

ADC ta yi martani ga fadar shugaban kasa, ta ce ta gama gigita APC

- Festus Keyamo.

Festus Keyamo ya ba Gwamna Mbah shawara

Keyamo ya kuma bukaci Gwamnatin Mbah ta tabbatar da cewa kamfanin Enugu Air ya kasance cikin tsarin kasuwanci mai inganci, ba tare da tsoma bakin siyasa ko tangarda daga ƴan siyasa ba.

A rahoton Channels tv, Keyamo ya ƙara da cewa:

"Abin da ya rage na shawara shi ne, kar a bar Enugu Air ya fada halin da tsohon kamfanin Nigerian Air ya fada.
"A tafiyar da shi da ƙwarewa, kada a bar siyasa ta hallaka Enugu Air. A tabbatar da cewa jirage na tashi da sauka akan lokaci.”
An kaddamar da kamfanin sufurim jirage na Enugu Air.
Keyawo ya bukaci a kaucewa sanya siyasa wajen tafiyar da Enugu Air Hoto: Peter Mbah
Source: Facebook

Kamfanin sufurin Enugu Air ya fara aiki

Kamfanin Enugu Air zai fara aiki da jirage guda uku na Embraer E170 da E190, wadanda aka zaɓa saboda sauƙin kula da su, jin daɗin fasinjoji, da dacewarsu da tafiye-tafiyen cikin ƙasa.

A ƙaron farko, jirgin zai fara jigilar fasinjoji daga Enugu zuwa jihohin Akwa Ibom, Abuja da Legas amma da yiwuwar a faɗaɗa shi zuwa Fatakwal, Owerro, Benin da Kano.

Kara karanta wannan

Wata sabuwa: Gwamnatin tarayya ta sanya jirgin shugaban kasa a kasuwa

Bukola Saraki ya gana da gwamnan Enugu

A wani rahoton, kun ji cewa tsohon shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki ya gana da Gwamna Peter Mbah da wasu jiga-jigan PDP a jihar Enugu.

Wannan taro wani ɓangare ne na ƙoƙarin da kwamitin da Saraki ke jagoranta domin farfaɗo da jam'iyyar PDP gabanin zaɓen 2027.

Saraki ya bayyana cewa sun tattauna batutuwa masu muhimmanci da suka addabi jam’iyyar, tare da fara tsara sababbin matakai domin dawo da martabar PDP.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262