"Ina Sha'awar Shiga APC saboda Mutum 2," Tsohon Hadimin Atiku Ya Yi Barazanar Barin PDP

"Ina Sha'awar Shiga APC saboda Mutum 2," Tsohon Hadimin Atiku Ya Yi Barazanar Barin PDP

  • Segun Showunmi ya bayyana cewa idan abubuwa suka ci gaba da lalacewa a jam'iyyar PDP, to zai tattara kayansa ya koma APC
  • Tsohon kakakin kwamitin kamfen PDP yana sha'awar shiga APC saboda yadda Bola Tinubu da Muhammadu Buhari suka zama tsayayyu
  • Ya ce saɓanin sauran manyan ƴan siyasa, Tinubu da Buhari sun tsaya ɓangare ɗaya ba tare da yawan sauya jam'iyyar siyasa ba

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Tsohon hadimin Atiku Abubakar, Segun Showunmi ya ce da yiwuwar ya sauya sheƙa daga jam'iyyar PDP zuwa APC mai mulkin Najeriya.

Mista Showunmi, tsohon mai magana da yawun kwamitin kamfen Atiku Abubakar a zaɓen 2023, ya ce zai bar PDP idan ya fahimci shugabannin jam'iyyar ba za su gyara ta ba.

Tsohon kakakin kwamitin kamfen PDP, Segun Sowunmi.
Sowunmi ya bayyana cewa zai iaya barin PDP idan abubuwa suka ci gaba da lalacewa Hoto: Segun Sowunmi
Source: Facebook

Jigon PDP ya bayyan haka ne a wata hira da aka yi da shi a cikin shirin 'Your View' na kafar watsa labarai ta TVC ranar Talata, 10 ga watan Yuni, 2025.

Kara karanta wannan

2027: Kusa a PDP ya ba Atiku shawara, ya fadi abin da zai koya wajen Tinubu

Kalaman Segun Showunmi na zuwa ne kwanaki ƙalilan bayan ya gana da shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu a gidansa da ke jihar Legas.

Tsohon hadimin Atiku na shirin barin PDP

Tsohon mai magana da yawun kwamitin kamfen Atiku a 2023 ya ce zai fice daga PDP idan shugabannin jam’iyyar suka nace wajen lalata ta.

Showunmi ya ce yana jin sha’awar shiga APC saboda yadda shugaban kasa Bola Tinubu da wanda ya gabace shi, Muhammadu Buhari, suka zama tsayayyun shugabanni.

A cewarsa:

"Bari ku ji, na sha faɗa kuma zan maimaita a yau, idan har na bar PDP to babu shakka APC zan shiga, kun san me yasa? Saboda ginshikan APC biyu, Bola Tinubu da Muhammadu Buhari tsayayyun mutane ne.
"Tinubu da Buhari ba su tsalle-tsallen sauya jam'iyyun siyasa, sun tsayu a tsagi ɗaya tun 1998."

Sowunmi ya faɗi alaƙarsa da kakakin APC na ƙasa

Kara karanta wannan

"Ba laifin Fubara ba ne," Yan Majalisa sun yi magana kan yiwuwar 'gwamna' ya koma APC

Showunmi ya ƙara da cewa idan har zai shiga APC, zai fara tuntubar abokinsa Felix Morka, mai magana da yawun APC na ƙasa, domin ya ji kundin tsarin jam'iyyar.

"Idan zan shiga APC, zan fara da ziyartar abokina Felix Morka. Zan zauna da shi, in nemi kundin tsarin mulki na jam’iyyar, in karanta shi," in ji shi.
Shugaba Tinubu da jigon PDP, Segun Sowunmi.
Sowunmi ya ce siyasar Bola Tinubu da Muhammadu Buhari tana burge shi Hoto: @officialABAT
Source: Facebook

Jigon PDP ya soki shirin haɗakar Atiku

Haka kuma, Showunmi ya nuna rashin amincewarsa da yunƙurin kafa haɗakar siyasa da Atiku ke jagoranta, yana mai cewa hakan ya kawo ruɗani a PDP.

A rahoton Vanguard, Showunmi ya ce:

“Ɗaya daga cikin abubuwan da ke damuna game da wannan magana ta haɗaka da ake yi ita ce ban ga dalilin da zai sa ‘yan siyasa na kirki su rika neman kafa sabon tsarin siyasa ba.

Ya kuma bayyana cewa ya shafe fiye da shekaru 27 a cikin PDP kuma ba zai ci gaba da jure rashin tabbas a jam’iyyar ba.

Sowunmi ya ɗora Tinubu a kan Obi da Atiku

A baya, kun ji cewa Segun Sowunmi ya yi ikirarin cewa shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya fi duka manyan masu adawa da shi a ƙasar nan dabara.

Kara karanta wannan

Tsohon na kusa da Atiku ya fadi fannin da Tinubu ya yi wa abokan hamayyarsa zarra

A cewar jigon na PDP, Shugaɓa Tinubu ya iya mu'amala da mutane yadda zai jawo ra'ayinsu, saɓanin abokan hamayyarsa irinsu Peter Obi.

Bugu da ƙari, ya yi bayani kan ziyarar da ya kaiwa Tinubu a Legas, yana mai cewa bai ci amanar alaƙarsa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262