2027: Atiku da Manyan 'Yan Siyasa 7 da Suka Dauki Aniyar Raba Tinubu da Ofis

2027: Atiku da Manyan 'Yan Siyasa 7 da Suka Dauki Aniyar Raba Tinubu da Ofis

Yayin da ‘yan Najeriya ke fama da hauhawar farashi da matsalolin tattalin arziki, siyasar 2027 ta fara daukar zafi ganin yadda manyan yan siyasa suka fara shirin babban zabe.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT Abuja – Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wanda ke cika shekaru biyu da fara mulkin Najeriya na fuskantar karuwar adawa daga fitattun ‘yan siyasa da ke neman hana APC komawa kujerar shugaban kasa.

Masu sukar gwamnatin na zargin Tinubu da aiwatar da manufofi marasa amfani, gazawa wajen rage radadin tattalin arziki, da kuma kokarin mayar da Najeriya mulkin jam’iyya daya.

Atiku
Manyan yan siyasa 8 sun sako gwamnatin Tinubu a gaba Hoto: @Omoluabi_sq
Source: Twitter

Jaridar Punch ta ruwaito cewa a yayin da jama’a ke nuna rashin jin dadi da gazawar manufofin gwamnati, wata hadaka ta manyan ‘yan siyasa na kunno kai, da burin kawar da Tinubu daga mulki a 2027.

Kara karanta wannan

'Akwai babbar barazana ga APC,' Babban lauya ya fadi abin da zai kifar da Tinubu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ana kokarin kawar da gwamnatin Tinubu

A cewar wasu jiga-jigan siyasa, ciki har da tsohon mataimakin shugaban kasa, gwamnati mai ci na kara jefa kasar cikin halin kunci, kamar yadda Atiku Abubakar ya bayyana a shafinsa na X.

Ba Atiku ne kadai ke da irin wannan ra'ayi ba, kamar yadda za a gani a jerin wasu daga cikin fitattun 'yan siyasa da ke kokarin hana Tinubu zarcewa mulki a 2027:

1. Atiku na jagorantar hadakar kifar da Tinubu

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, wanda ya tsaya takara a karkashin PDP a 2023, bai nuna wata alamar janyewa daga siyasa ba.

Atiku Abubakar da hadin gwiwar wasu manyan yan siyasa sun kirkiro hadakar adawa da za a taru a ciki domin tabbatar da cewa APC ba ta koma shugabancin Najeriya a 2027 ba.

Atiku
Atiku na daga cikin masu jagorantar hadakar adawa Hoto: Atiku Abubakar
Source: Facebook

Rahotanni na nuna cewa akwai yiwuwar Atiku ya mika tayin yin wa’adi daya na shugabanci tare da Peter Obi a matsayin mataimakinsa, don hada karfi da karfe a zaben 2027.

Kara karanta wannan

'Mutum sama da 10,000 aka yiwa kisan gilla a mulkin Tinubu," Amnesty Int'l

Har yanzu, hadakar adawar da aka kafa tana shawarwari a kan matsayar da za a cimma.

2. Peter Obi na adawa da gwamnatin Tinubu

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, ya bayyana cewa ta yiwu ba zai sake tsayawa takara a 2027, amma yana tare da hadakar ceto talaka.

Obi na ci gaba da bayyana bukatarsa ta sauya salon siyasar Najeriya, tare da shirin kafa hadaka da wasu manyan ‘yan siyasa.

Peter Obi
Peter Obi na daga cikin masu adawa da gwamnatin Tinubu Hoto: Mr. Peter Obi
Source: Twitter

A watan Maris, Obi ya hada kai da Atiku Abubakar da Nasir El-Rufa'i domin kafa wata sabuwar hadaka da za ta kalubalanci Tinubu a zaben da ke tafe.

Wasu rahotanni ma sun nuna yiwuwar Obi zai amince da matsayin mataimaki ga Atiku karkashin yarjejeniyar wa’adi daya, duk da cewa ba daya daga cikinsu ya tabbatar da hakan ba.

3. El-Rufa'i na kalubalantar gwamantin APC

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i, na daga cikin masu sukar gwamnatin Bola Tinubu da suka fi bayyana rashin gamsuwarsu da tsarin da ake kai.

Kara karanta wannan

2027: Sanatoci sun gano dalilin kara karfin Boko Haram da sauran 'yan ta'adda

A wata ganawa a watan Mayu, El-Rufai ya ce:

“Duk wanda ke ganin Tinubu zai iya komawa mulki a 2027 yana zaune a wata kasa daban, ba Najeriya ba."

El-Rufai ya ce halin da tattalin arzikin kasa ke ciki a yanzu, da tsarin siyasarsa ya sa Tinubu ya rasa goyon bayan jama’a.

4. Seyi Makinde na son karbar mulki

A watan Afrilu, gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya bayyana cewa yana da kwarewar jagorantar Najeriya, kodayake ya ce zai duba ra’ayin ‘yan Najeriya da jam’iyyarsa kafin batun takara.

Seyi Makinde
Gwamnan Oyo na daga cikin wadanda ke ganin sun cancanci shugabancin Najeriya Hoto: Seyi Makinde
Source: Facebook

Ya ce:

“Babu shakka ina da kwarewar jagorantar kasar nan… amma abin da nake so in yi yanzu, shin shi ne abin da ‘yan Najeriya ke bukata?”

Gwamnan, wanda ke daga cikin 'yan adawa masu rajin kishin jam'iyyarsa ta PDP ya kara da bayyana cewa babu shakka, ana bukatar sauyi a kasar nan.

5. Babachir ya fusata da salon mulkin Tinubu

Babachir Lawal, tsohon sakataren gwamnatin tarayya, na daga cikin fitattun masu adawa da gwamnatin Bola Tinubu.

Kara karanta wannan

Atiku ya tono manyan 'kurakuran' Tinubu a shekara 2, ya yi raddi mai zafi

Lawal na taka muhimmiyar rawa wajen tsara dabarun hadakar siyasa da ke shirin kalubalantar Tinubu a 2027.

Babachir
Babachir Lawal na ganin gwamnatin Bola Tinubu ta gaza Hoto: @babachirlawal
Source: Twitter

Ya sha nanata cewa an kai matakin fahimtar juna a hadakar, kuma ba sa bukatar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya sa albarka kafin a barar da gwamnatin APC.

6. Amaechi da Imoke na adawa da gwamnati

Tsofaffin gwamnonin jihohin Ribas da Kuros Riba, Rotimi Amaechi da Liyel Imoke, na cikin masu tsara dandalin siyasa da hadakar za ta yi amfani da shi wajen korar Tinubu daga ofis.

Rotimi
Rotimi Amaechi na daga cikin jiga-jigan hadakar adawa da Tinubu Hoto: Rotimi Amaechi
Source: Facebook

Amaechi na jagorantar kwamitin da ke duba yiwuwar rajistar sabuwar jam’iyya, yayin da Imoke ke jagorantar bangaren da ke nazarin hadin gwiwa da jam’iyyun da suka riga suna kasa.

Imoke
Tsohon gwamnan Kuros Riba na jagorantar wani kwamiti a hadakar adawa da Tinubu Hoto: Liyel Imoke
Source: Facebook

7. Nwosu na ganin ADC za ta ja da Tinubu

Shugaban jam’iyyar ADC, Ralph Okey Nwosu, ya yi watsi da ra’ayin cewa ba za a iya kayar da Tinubu a 2027 ba.

A wata hira da aka yi da shi kwanan nan, Nwosu ya ce daga Legas zuwa Fatakwal, Kano, Uyo, da Sakkwato, talauci da rashin tsaro sun hada kan ‘yan Najeriya.

Kara karanta wannan

Bayanin da Bola Tinubu ya yi wa Najeriya bayan cika shekara 2 a kan mulki

Ya bayyana cewa matsalolin da ake fama da su sun bayyana gazawar gwamnatin Bola Tinubu wajen hana ci gaban Najeriya.

Ya ce:

“Talauci da rashin tsaro da gwamnatin APC ta jawo suna cinye kasar nan. Gwamnatin APC ta gaza matuka… APC a matsayin jam’iyya ta wuce kima.”

Atiku ya soki mulkin Tinubu

A baya, kun ji cewa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya sake caccakar gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana zargin ta gaza cika alkawari.

Atiku, wanda ke wannan batu bayan Shugaba Bola Tinubu ya shekara biyu a karagar mulki ya ce gwamnati na kara jefa ‘yan Najeriya cikin kunci da talauci, da halin ni 'ya su.

Ya kara da cewa gwamnatin Tinubu ta ci amanar ‘yan kasa tare da gazawa wajen cika alkawurran da ta dauka a lokacin yakin neman zabe na inganta rayuwarsu.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng