PDP Ta Sha Kaye, Kotun Daukaka Ƙara Ta Yanke Hukunci a Karar da Aka Nemi Tsige Gwamna

PDP Ta Sha Kaye, Kotun Daukaka Ƙara Ta Yanke Hukunci a Karar da Aka Nemi Tsige Gwamna

  • Gwamna Monday Okpebholo ya sake doke babban abokin hamayyarsa na PDP, Asue Ighodalo a kotun ɗaukaka ƙara mai zama a Abuja
  • A hukuncin da ta yanke yau Alhamis, kotun ta tabbatar da nasarar jam'iyyar APC a zaben gwamnan jihar Edo da aka yi a watan Satumba, 2024
  • Sai dai duk da haka ɗan takarar jam'iyyar PDP, Ighodalo bai haƙura ba, ya sha alwashin sake ɗaukaka kara zuwa kotun kolin Najeriya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Edo - Kotun Daukaka Kara mai zama a Abuja ta tabbatar da nasarar Gwamna Monday Okpebholo na jihar Edo a zaben da aka yi ranar 21 ga Satumba, 2024.

Hakan dai na kunshe ne a hukuncin da kwamitin alkalan kotun mai mutum uku karkashin jagorancin Mai Shari’a M. A. Danjuma ya yanke yau Alhamis a Abuja.

Kara karanta wannan

Bayan sanin makomarsa a kotu, gwamnan Edo ya aika sako ga abokin hamayyarsa

Asue Ighodalo.
Kotun ɗaukaka kara ta tabbatar da nasarar APC a zaben gwamnan jihar Edo Hoto: @Aighodalo, @M_Akpakomiza
Source: Facebook

Gwamna Monday Okpebholo ya sake doke PDP

Jaridar Vanguard ta rahoto cewa kotun ta yi watsi da karar da jam’iyyar PDP da dan takararta, Asuerinme Ighodalo, suka shigar domin kalubalantar sakamakon zaben.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kotun ta ce babu wani dalili da zai sa a rushe hukuncin da kotun sauraron ƙararrakin zaben gwamnan Edo ta yanke, wanda ya tabbatar da Gwamna Okpebholo na APC a matsayin wanda ya lashe zaben.

A baya, kotun zaɓe karkashin jagorancin Mai Shari’a Wilfred Kpochi ta yi watsi da ƙorafe-ƙorafen PDP da dan takararta; jam’iyyar AA da shugabanta na kasa, Adekunle Rufai Omoaje; da AP tare da dan takararta, Dr. Bright Enabulele.

Yadda shari'ar ta gudana a kotun zaɓen Edo

Kotun ta ce babu gamsasshen dalili da zai sa a soke sakamakon da INEC ta bayyana wanda ya ba Okpebholo na APC nasara da kuri’u 291,667.

Gwamna Okpebholo ya samu nasarar kayar da babban abokin hamayyarsa, dan takarar PDP, Ighodalo, wanda ya samu ƙuri'u 247,655.

Kara karanta wannan

Gwamna zai san makomarsa a yau, da yiwuwar kotun ɗaukaka ƙara ta tsige shi

PDP da Ighodalo sun kalubalanci sakamakon zaben da cewa an tafka kura-kurai, magudi, da kuma cewa zaben ya gudana ba kan ka’idojin dokar zabe ta 2022 ba.

Sun kuma zargi INEC da rashin sarrafa kayayyakin zabe yadda ya kamata, musamman batun rashin sanya lambobi a wasu kayan zabe masu muhimmanci, lamarin da suka ce ya taimaka wajen sauya sakamakon zaben.

Masu karar sun gabatar da shaidu 19 tare da hujjoji, inda suka ce an samu kuskuren kidayar kuri’u a rumfunan zabe 765.

Gwamna Okpebholo.
Kotun daukaka kara ta ce babu dalilin da zai a sauke gwamnan Edo daga mulki Hoto: Monday Okpebholo
Source: Facebook

Zaɓen Edo: Wane hukunci kotu ta yanke?

Da take yanke hukunci, kotun zaɓe ta ce PDP da dan takararta sun kasa gabatar da kwakkwaran shaida da za ta sa a rushe sakamakon zaben.

A yau Alhamis kuma, Kotun Daukaka Kara da ke zamanta a Abuja ta tabbatar da hukuncin kotun zaɓe, kamar yadda jaridar The Nation ta rahoto.

A gefe guda, Asuerinme Ighodalo ya bayyana cewa zai daukaka kara zuwa Kotun Koli, wadda ke da hurumin yanke hukuncin karshe kan shari’ar zaben.

Gwamnan Edo ya yi ƙarin albashi

A wani rahoton, kun ji cewa Gwamna Monday Okpebholo ya amince da ɗaga sabon mafi karancin albashi zuwa ₦75,000 ga ma’aikatan jihar Edo.

Kara karanta wannan

NEC: Atiku, Wike da wasu jiga jigan PDP sun yi watsi da babban taron jam'iyya

Ya ce wannan ƙari wata hanya ce ta nuna godiya ga ma’aikatan gwamnatin jihar, tare da fatan za su ƙara himma wajen ganin Edo ta ci gaba.

Gwamna Okpebholo ya kara da cewa gwamnatinsa ta ɗauki lamarin walwala da jin daɗin ma'aikata da matuƙar muhimmanci tun daga lokacin da ya hau mulki.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262