Dan Majalisa a Arewa Zai Hada kan Yarbawa a Yankin domin Zaben Tinubu a 2027

Dan Majalisa a Arewa Zai Hada kan Yarbawa a Yankin domin Zaben Tinubu a 2027

  • Dan majalisar wakilai, Hon. Leke Abejide ya bukaci hadin kan Yarbawa a yankin kan zaben 2027
  • Hon. Abejide ya bukaci shugabannin Yarbawa a Arewa su marawa Bola Tinubu baya a takararsa ta 2027 don ci gaban al'umma
  • A taron cika shekara 10 na shugabannin gargajiya na Yarbawa a Arewa, Abejide ya jaddada muhimmancin hadin kai da gujewa siyasar rarrabuwar kawuna
  • Ya kuma kaddamar da aikin hanya mai tsawon kilomita 57.2 da gina fada na zamani a Kano domin karfafa tasirin Yarbawa da ci gaban al'umma

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Tsohon dan takarar gwamna na ADC a Kogi, Hon. Leke Abejide, ya bukaci shugabannin Yarbawa a Arewa su marawa Tinubu baya a takararsa ta 2027.

Hon. Abejide wanda dan majalisar wakilai ne daga jihar Kogi ya ce hadin kai yana da matukar muhimmanci.

Kara karanta wannan

Shugabannin Arewa sun yiwa Ganduje kaca kaca, sun kalubalanci tazarcen Tinubu

Dan Ya roki Yarbawan Arewa kan goyon bayan Tinubu a 2027
Hon. Abejide Leke ya bukaci hadin kan Yarbawa a Arewa domin zaɓen Tinubu a 2027. Hoto: Hon. Leke Abejide, Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

Asiwajun Yarbawa a Kano ya magantu kan zabe

A taron cika shekara 10 na Kungiyar Sarakunan Gargajiya na Yarbawa a Arewa da FCT, Abejide ya bukaci hadin kai da gujewa siyasar rarrabuwar kawuna, cewar Leadership.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Abejide wanda shi ne Asiwaju na Yarbawa a Kano, ya jaddada cewa hadin kan Yarbawa yana da matukar muhimmanci wajen samun tasiri a kasa da ci gaban al'umma.

“Yarbawa suna da yawa a Najeriya, idan aka cire su, giɓi zai bayyana sosai, don haka, dole mu kasance tare."
“Zan taimaka muku idan muka hada kai wajen goyon bayan Shugaban kasa, tasirinku a al'umma zai taimaka wajen cimma wannan buri."

- Hon. Leke Abejide

Dan Majalisa ya gina hanya a Kano

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Yagba, Abejide, ya ba da tabbacin goyon bayansa ga ci gaban kungiyar da bunkasa al'ummomin Yarbawa a Arewa.

Ya sanar da gina hanya mai tsawon kilomita 57.2 da kuma shirin gina fada na zamani a Kano don karfafa tasirin Yarbawa a Arewa.

Kara karanta wannan

Dandazon jama'a sun tarbi Buhari da ya fito zabe na farko bayan gama mulki

Shugaban sabuwar kwamitin shugabanni, Muritala Adeleke, ya sha alwashin hada kan Yarbawa da bunkasa shirye-shiryen tattalin arziki ga al'ummomin Yarbawa a Arewa.

Dan Majalisa ya bukaci fassara kudirin haraji da Hausa

Kun ji cewa wani dan majalisar wakilai daga jihar Kogi, Hon. Leke Abejide ya bukaci a fassara kudirin haraji zuwa harshen Hausa.

Hon. Leke ya shawarci fassara kudirin zuwa harshen Hausa duba da yadda matsalar ta fi yawa a Arewacin Najeriya saboda a fi fahimtar lamarin da kyau.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.