APC Ta Shawarci El Rufa'i a Kawo Ƙarshen Takun Saka da Gwamnatin Tinubu

APC Ta Shawarci El Rufa'i a Kawo Ƙarshen Takun Saka da Gwamnatin Tinubu

  • APC ta Kano ta tabbatar da tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa’i, ya bayar da gudunmawa a nasarar Bola Ahmed Tinubu a zaben 2023
  • Wannan na zuwa ne duk da rashin jituwar da ke tsakanin tsohon gwamnan da gwamnatin tarayya, har ya ke ganin ana barazanar cafke shi
  • Sakataren yada labaran APC na Kano, Ahmed S Aruwan ya shaida wa Legit cewa lokaci ya yi da El-Rufa’i zai tuna matsayinsa don yin sulhu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar KanoJam'iyyar APC ta tabbatar da cewa tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa'i ya bayar da gudunmawa wajen samar da nasarar shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a zaben 2023.

Sakataren yada labaran APC, Ahmed S Aruwan da ya bayyana hakan ga Legit, ya kara da cewa ba sa jin dadin takun saka da ya shiga tsakanin tsohon gwamnan da gwamnatin tarayya.

Kara karanta wannan

Yadda gwamnatin tarayya ta nemi ba ni rashawar N5bn," Ɗan takarar shugaban ƙasa

Tinubu
APC ta nemi El-Rufa'i ya sasanta da jam'iyyarsa Hoto: Bayo Onanuga/Abdullahi Ganduje/Nasir El-Rufa'i
Asali: Facebook

Kakakin jam'iyyar yake cewa amma wannan ba ya nufin suna goyon bayan yadda El-Rufa'i ke kokarin tadiye APC ta cikin gida, domin za a iya magance dukkanin koken da ya ke da su a cikin ruwan sanyi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An yi hasashen matsalar Nasir El-Rufa'i da APC

Ahmad Aruwan ya bayyana cewa bai cika son magana a kan tsohon gwamnan Kaduna, El-Rufa'i ba, ganin cewa har yanzu ba a gama tantance menene damuwarsa da jam'iyya ba.

Ya bayyana cewa:

"Na san da an kai sunansa a matsayin wanda za a yi wa Minista, daga karshe aka zo aka janye. Mai yiwuwa ba ya rasa nasaba da siyasarsu a Kaduna. Ba ya rasa nasaba da gwamnatinsu ta Kaduna da wanda ya gaje shi.
Wata rigimar daga cikin gida ta ke, daga gidanka ne za a tadiye ka, daga gidanka ne za a ce ba a sonka, daga gidanka ne za a yi maka bita da kulli idan ma ita ce.

Kara karanta wannan

"Tinubu zai sha wahala": LP ta bayyana wanda za ta tsayar takarar shugaban ƙasa a 2027

APC ta nemi El-Rufa'i ya zauna da Tinubu

APC ta tunatar da Nasir El-Rufa'i matsayinsa a siyasar Najeriya, da yadda ya taka rawa wajen samun nasarar jam'iyyar, tun daga lokacin Muhammadu Buhari zuwa Bola Tinubu.

Ahmed S Aruwan ya ce:

"Sai ka yi hakuri, sai ka zauna da jam'iyyarka, idan ma akwai matsala zai iya ganin shugaban kasa, zai iya ganin shugaban jam'iyya, a duba lamarin. Menene ya faru? Me ake ciki? Menene matsalarmu? Me mu ka yi? Menene laifin mu?

Ya kara da cewa da El-Rufa'i aka gina APC, saboda haka ya yi hakuri wajen neman a yi sulhun siyasa da jam'iyyar APC, domin ba za a iya goge tarihinsa a jam'iyyar ba.

El-Rufa'i ya yi magana kan shirin kama shi

A baya, mun ruwaito cewa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i ya bayyana cewa ba tun yanzu ya ke samun labarin cewa gwamnatin tarayya na shirin cafke shi ba saboda adawa da ita.

Kara karanta wannan

Arewa: El-Rufa'i ya aika gargadi ga APC da Tinubu kan zaben 2027

El-Rufa'i ya ce amma wannan barazanar ba za ta ba shi tsoro ba, ganin cewa shi dan gwagwarmaya ne a siyasa da ya dade ya na fuskantar makamancin wannan barazana daga gwamnatocin baya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.

iiq_pixel