Kwankwaso Ya Gana da Tsohon Gwamnan APC, an Yi Hasashen Shirin Tumbuke Tinubu

Kwankwaso Ya Gana da Tsohon Gwamnan APC, an Yi Hasashen Shirin Tumbuke Tinubu

  • Tsohon gwamnan Osun, Rauf Aregbesola da Rabiu Kwankwaso sun gana a Legas da ake zargin bai rasa nasaba na zaben 2027
  • Ganawar ta kasance mai tsawo inda jiga-jigan siyasar suka tattauna batutuwa masu muhimmanci game da makomar siyasa a Najeriya
  • Ana sa ran karin bayani daga bangarorin da suka halarci wannan ganawa, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen babban zaben kasa
  • Wannan na zuwa ne yayin da wasu ke hasashen hadakar jam'iyyun adawa da matsalar Aregbesola da APC

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Ikeja, Lagos - Tsohon gwamnan Osun, Rauf Aregbesola ya yi muhimmiyar ganawa da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Tsohon ministan harkokin cikin gida da Rabiu Kwankwaso sun gana a Lagos domin “tsara dabaru” kafin zaben 2027.

Kwankwaso ya gana da tsohon gwamna a APC
Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya gana da Rauf Aregbesola a Lagos. Hoto: Rabiu Musa Kwankwaso, Rauf Aregbesola.
Asali: Twitter

APC ta kori Aregbesola daga jam'iyyar

Kara karanta wannan

Shugaban NNPP ya tabbatar da korar Kwankwaso da Buba Galadima a jam'iyya

TheCable ta tabbatar da cewa wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa an yi ganawar saboda zaben 2027 mai zuwa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wannan na zuwa ne bayan jam'iyyar APC ta kori tsohon gwamnan na jihar Osun bisa zargin cin dunduniyarta da kuma wasu zarge-zarge da ake yi masa.

Kwamitin gudanarwa na APC na Osun ya ce an ɗauki matakin korar Aregbesola ne bayan samun rahoto kan binciken da aka yi a kansa.

2027: Kwankwaso ya gana da Aregbesola a Lagos

An gudanar da taron a yau Asabar 8 ga watan Janairun 2025 wanda aka shafe fiye da awa daya ana ganawar a Lagos, cewar The Guardian.

Duk da yake ba a fitar da cikakkun bayanai ga manema labarai ba, majiyoyi sun ce hakan na da alaka da shirin shiga jam’iyyar NNPP da Aregbesola da magoya bayansa ke yi.

A kwanakin baya, an yi ta rade-radin cewa Aregbesola da magoya bayansa na iya komawa NNPP kafin zaɓen gwamnan Osun na badi.

Kara karanta wannan

'Yar hassada ce': Musa Kwankwaso ya soki Naja'atu, ya jero manyan da ta zaga

“Aregbesola da Kwankwaso sun gama wani dogon taro a Lagos inda suka tsara dabarun zaben 2027."

- Cewar wata majiya

Tsohon kwamishinan Ganduje ya koma layin Kwankwaso

Kun ji cewa tsohon kwamishinan shari'a a gwamnatin Abdullahi Ganduje, Barista Haruna Isah Falali, ya sauya sheƙa zuwa jam'iyyar NNPP.

Jagoran jam'iyyar NNPP na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, ya karɓi Haruna Isa Falali da kansa a gidansa da ke Abuja.

Yan Kwankwasiyya sun nuna farin ciki da shigowar Falali jam'iyyarsu, suna addu'ar hakan ya haifar da nasara a tafiyarsu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

iiq_pixel