Kwankwaso Ya Gana da Tsohon Gwamnan APC, an Yi Hasashen Shirin Tumbuke Tinubu
- Tsohon gwamnan Osun, Rauf Aregbesola da Rabiu Kwankwaso sun gana a Legas da ake zargin bai rasa nasaba na zaben 2027
- Ganawar ta kasance mai tsawo inda jiga-jigan siyasar suka tattauna batutuwa masu muhimmanci game da makomar siyasa a Najeriya
- Ana sa ran karin bayani daga bangarorin da suka halarci wannan ganawa, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen babban zaben kasa
- Wannan na zuwa ne yayin da wasu ke hasashen hadakar jam'iyyun adawa da matsalar Aregbesola da APC
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Ikeja, Lagos - Tsohon gwamnan Osun, Rauf Aregbesola ya yi muhimmiyar ganawa da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.
Tsohon ministan harkokin cikin gida da Rabiu Kwankwaso sun gana a Lagos domin “tsara dabaru” kafin zaben 2027.

Asali: Twitter
APC ta kori Aregbesola daga jam'iyyar
TheCable ta tabbatar da cewa wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa an yi ganawar saboda zaben 2027 mai zuwa.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Wannan na zuwa ne bayan jam'iyyar APC ta kori tsohon gwamnan na jihar Osun bisa zargin cin dunduniyarta da kuma wasu zarge-zarge da ake yi masa.
Kwamitin gudanarwa na APC na Osun ya ce an ɗauki matakin korar Aregbesola ne bayan samun rahoto kan binciken da aka yi a kansa.
2027: Kwankwaso ya gana da Aregbesola a Lagos
An gudanar da taron a yau Asabar 8 ga watan Janairun 2025 wanda aka shafe fiye da awa daya ana ganawar a Lagos, cewar The Guardian.
Duk da yake ba a fitar da cikakkun bayanai ga manema labarai ba, majiyoyi sun ce hakan na da alaka da shirin shiga jam’iyyar NNPP da Aregbesola da magoya bayansa ke yi.
A kwanakin baya, an yi ta rade-radin cewa Aregbesola da magoya bayansa na iya komawa NNPP kafin zaɓen gwamnan Osun na badi.
“Aregbesola da Kwankwaso sun gama wani dogon taro a Lagos inda suka tsara dabarun zaben 2027."
- Cewar wata majiya
Tsohon kwamishinan Ganduje ya koma layin Kwankwaso
Kun ji cewa tsohon kwamishinan shari'a a gwamnatin Abdullahi Ganduje, Barista Haruna Isah Falali, ya sauya sheƙa zuwa jam'iyyar NNPP.
Jagoran jam'iyyar NNPP na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, ya karɓi Haruna Isa Falali da kansa a gidansa da ke Abuja.
Yan Kwankwasiyya sun nuna farin ciki da shigowar Falali jam'iyyarsu, suna addu'ar hakan ya haifar da nasara a tafiyarsu.
Asali: Legit.ng