Bidiyo: Fusatattun Matasa Sun Lalata Manyan Allunan Hotunan Tinubu a Yobe

Bidiyo: Fusatattun Matasa Sun Lalata Manyan Allunan Hotunan Tinubu a Yobe

  • Fusatattun matasan jihar Yobe sun lalata manyan allunan kan titi ɗauke da hotunan Tinubu, Shettima da Gwamna Buni
  • An kafa allunan ne domin maraba da shugaban ƙasar zuwa ƙaddamar shirin karfafa noma da kiwo a jihar Yobe
  • Sai dai, matasan sun ɗare kan allunan a wani bidiyo tare da fatattaka hotunan da ke ɗauke da sakon godiya da fatan sauka lafiya ga Tinubu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Damaturu, Yobe - Wasu fusatattun matasa a Damaturu, babban birnin jihar Yobe, sun lalata manyan allunan da aka kafa domin yi wa Shugaba Bola Tinubu maraba zuwa jihar.

A ranar Asabar, mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima, ya wakilci Shugaba Tinubu wurin ƙaddamar da wani shirin ƙarfafa noma a Yobe da aka yi a Damaturu.

Kara karanta wannan

Malamin addini ya bayyana yadda Tinubu ya jefa 'yan Najeriya cikin wuya, ya ba shi mafita

Matasa sun sauke alluna dauke da hoton Tinubu a jihar Yobe
Matasan jihar Yobe sun lalata allunan sanarwar zuwan Tinubu jihar. Hoto: @officialABAT
Asali: Twitter

"Muhimmancin noma a Najeriya" - Tinubu

A cewar Shugaba Tinubu, shirin babban abu ne a mulkinsa a ƙoƙarin inganta tsaron abinci, samar da ayyuka da faɗaɗa tattalin arzikin Najeriya ta hanyar noma, Daily Trust ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaban ƙasar ya jaddada muhimmiyar rawar da noma yake takawa a cigaban ƙasa da tsaro, inda yace:

"Abinci shi ne ginshiƙin tsaro a kowacce al'umma. Shi ne ginshiƙin da ake gina lafiya a kai, walwala da daidaituwar tattalin arziki.
"Babu yadda za a yi mu cimma manufofinmu a matsayin gwamnati, a matakin jiha ko ƙasa, har sai da taimakon manomanmu."

Yobe: Matasa sun yago fastocin Tinubu

Sai dai, bayan kaddamar da shirin, an ga matasa a jihar a wani bidiyo da ya yaɗu suna hawa kan allunan dake ɗauke da hotunan Shugaba Tinubu, mataimakinsa Shettima da Gwamna Mai Mala Buni.

Kara karanta wannan

Zanga zangar adawa da Tinubu ta samu cikas bayan wasu matasan Arewa sun fice

"Mun gode Shugaban ƙasa. Allah ya kiyaye."

- Aka rubuta a jikin allon.

Fusatattun matasan sun lalata allunan tare da sauke hotunan dake ɗauke da sakon zuwa kasa.

Kalli bidiyon a kasa kamar yadda Nigeria Stories suka wallafa a X:

An garkame matashin mai kiran zanga-zanga

A wani labari na daban, mun ruwaito cewa, matashin nan da yayi kira da a bankado malamai daga kan mumbari matukar suka hana zanga-zanga, mai suna Junaidu Abdullahi, yana gidan kurkuku.

Junaidu wanda aka fi sani da AbuSalma, yayi batan dabo bayan kwanaki da ya saki bidiyon bore ga malamai masu hana yin zanga-zanga.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.