"Jam'iyyar APC Ta Shirya Ƙwace Kujerar Gwamnan PDP a 2024," Sanata Ya Magantu

"Jam'iyyar APC Ta Shirya Ƙwace Kujerar Gwamnan PDP a 2024," Sanata Ya Magantu

  • Tsohon gwamnan Edo, Sanata Adams Oshiomhole ya ce APC ta kammala shirye-shiryen tunkarar zaɓen gwamna a watan Satumba, 2024
  • Sanata mai wakiltar Edo ta Arewa ya ce jam'iyyar ta kudiri aniyar ƙwace kujerar gwamna daga hannun jam'iyyar PDP
  • Darakta Janar na kwamitin kamfen APC ya buƙaci dukkan mambobin jam'iyyar su haɗa kai su yi aiki tare domin samun nasara a zaɓe mai zuwa

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Edo - Sanata mai wakiltar Edo ta Arewa, Adams Oshiomhole, ya bayyana cewa jam'iyyar APC ta shirya kwace kujerar gwamnan jihar a zaɓen da ke tafe.

Sanata Oshiomhole ya faɗi haka ne ranar Jumu'a a wurin kaddamar da kwamitin yaƙin neman zaɓen jam'iyyar APC.

Kara karanta wannan

Mataimakin gwamnan da aka tsige da ɗan majalisar tarayya sun koma bayan APC

Adams Oshiomhole
Jam'iyyar APC ta shirya lashe zaɓen gwamna a jihar Edo Hoto: Adams Oshiomhole
Asali: Facebook

Kamar yadda Channels tv ta tattaro, hukumar zaɓe INEC ta tsara gudanar da zaɓen gwamna a jihar Edo ranar 21 ga watan Satumba, 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Taya APC zata lashe zaɓen Edo?

Da yake jawabi a taron, Oshiomhole wanda kuma tsohon gwamnan Edo ne, ya tabbatar da cewa jam’iyyar ta kuduri aniyar lashe zaben ta hanyar dimokradiyya.

“Muna so mu ci zabe ta hanyar dimokradiyya, ba mago mago, ba wuru-wuru, babu maguɗi ko tashin hankali.
"Muna fafutukar ganin mun sauya gwamnati cikin lumana, abin da dimokuradiyya ke nufi kenan,” in ji shi.

Shugaban kamfe ya nemi haɗin kai

A nasa jawabin, Darakta Janar na tawagar yakin neman zaben, Sanata Matthew Uroghide ya jaddada cewa dukkan ‘ya’yan jam’iyyar suna da muhimmanci.

Ya buƙaci mambobin APC da su sa a ransu suna kan manufa ɗaya ne da suke son cimma wa ko da kuwa babu sunayensu a cikin tawagar yaƙin neman zaɓe.

Kara karanta wannan

Ana daf da zaɓe, ƙanin Gwamna ya watsa masa ƙasa a ido, ya bar jam'iyyar PDP

Ya kuma tabbatar da cewa ƙofarsa a buɗe take na ya zauna ya saurari koke ko tambayoyi daga kowane mamba dangane da kamfen da za a fara gadan-gadan.

A rahoton Vanguard, Daraktan Kamfen ya ce:

"Don Allah mu yi aiki tare, ya zama dole mu yi aiki tare. idan akwai wata matsala ta jam'iyya ko kamfe ku zo ku same ni, kowa yana da muhimmanci."

APC ta samu ƙarin goyon baya

A wani rahoton na daban mataimakin gwamnan jihar Edo da aka tsige, Philip Shaibu da tsohon ɗan majalisar tarayya sun koma bayan jam'iyyar APC.

Manyan jiga-jigan biyu sun bayar da gudummuwa mai tsoka ga kwamitin yaƙin neman zaɓen ɗan takarar APC, Monday Okpebolo.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel