Kashim Shettima Ya Bayyana Yadda Tinubu Ya Gina Atiku da Sauran Mutane a Siyasa
- Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima ya bayyana Bola Tinubu a matsayin gwarzo a tarihin dimokuraɗiyyar Najeriya
- Sanata Kashim Shettima ya fadi haka ne yayin da yake bayyana irin yadda shugaba Tinubu ya taimakawa yan siyasar Kudu da Arewa
- Cikin waɗanda Kashim Shettima ya ambata har da Atiku Abubakar wanda shi ne babban abokin hamayyar shugaba Bola Tinubu a yanzu
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Nigeria - Mataimakin shugaban kasa Sanata Kashim Shettima ya siffanta shugaban kasa Bola Tinubu a matsayin gwarzon dimokuraɗiyya a Najeriya.
Sanata Kashim Shettima ya faɗi haka ne ganin yadda shugaban kasar ya dauki shekaru yana taimakon yan siyasa a kasar.
![](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/2aa884bea9fa01d7.jpg?impolicy=cropped-image&imwidth=256)
Kara karanta wannan
"Ina fatan lafiya": Atiku ya magantu bayan Tinubu ya zame har kasa a faifan bidiyo
![Kashim Shettima Kashim Shettima](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/21def84d03236b5a.jpg?imwidth=900)
Asali: Facebook
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa mataimakin shugaban kasar ya yi jawabin ne a lokacin wani taro da aka shirya domin murnar ranar dimokuraɗiyya a Najeriya.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Shettima: "Tinubu mafaka ne ga 'yan adawa"
Sanata Kashim Shettima ya bayyana cewa ba za a taɓa mantawa da Bola Tinubu ba a tarihin jam'iyyun adawa a Najeriya.
Shettima ya ce a Bola Tinubu ya zama bango ne da dukkan ƴan adawa ke jingina da shi a lokacin mulkin PDP kuma ya yaki tsarin kafa jam'iyya daya a kasar.
'Yan siyasan da Bola Tinubu ya gina
Mataimakin shugaban kasar ya bayyana cewa Bola Tinubu ya gina yan siyasa da dama a dukkan bangarorin Najeriya, rahoton Daily Post.
Cikin manyan yan siyasa da Tinubu ya taimaka Shettima ya ambaci Atiku Abubakar, Olusegun Mimiko, Rauf Aregbesola da Adams Oshimole.
![](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/d9c39af4af0bc7b3.jpg?impolicy=cropped-image&imwidth=256)
Kara karanta wannan
Tinubu ya faɗi ƙasa yayin taron ranar dimokuraɗiyya, fadar shugaban ƙasa ta yi martani
Tinubu ya ba Atiku Abubakar takara
Har ila yau Kashim Shettima ya ce a lokacin da aka kori Atiku Abubakar daga PDP wajen Bola Tinubu yaje neman mafita.
Ya ce a lokacin Bola Tinubu ya karbi Atiku Abubakar hannu biyu biyu har ma ya ba shi damar tsayawa takara a jam'iyyar AC.
Shettima ya fasa tafiya Amurka
A wani rahoton, kun ji cewa Kashim Shettima ya fasa tafiyar da aka tsara zai wakilci shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu a taron kuwanci a Dallas.
Mataimakin shugaban ƙasar ya soke wannan tafiya ne sakamakon wata tangarɗa da jirginsa ya samu, ministan waje ne ya wakilci Tinubu a taron.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng