Osun: Ruɗani Yayin da 'First Lady' 2 Suka Bayyana Wajen Tarbar Remi Tinubu, an Samu Mafita

Osun: Ruɗani Yayin da 'First Lady' 2 Suka Bayyana Wajen Tarbar Remi Tinubu, an Samu Mafita

  • An shiga rudani bayan samun 'First Lady' guda biyu a jihar Osun yayin tarbar matar shugaban kasa, Sanata Remi Tinubu
  • An gano wasu takardu da ke yawo inda suke tarbar Remi zuwa jihar daga ofisoshin dukkan matan gwamnan guda biyu
  • Daga bisani gwamnatin jihar ta fitar da sanarwa inda ta fayyace asalin 'First Lady' a jihar wacce za ta tarbi Remi Tinubu

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Osun - An ga hatsaniya a jihar Osun yayin da matan Gwamna Ademola Adeleke suke shirye-shiryen tarbar matar shugaban kasa, Remi Tinubu.

Matan guda biyu dukkansu sun buga takardun tarbar matar shugaban kasa, Bola Tinubu.

Kara karanta wannan

"Tinubu ya dara su", Jigon APC ya fadi yadda Najeriya za ta kasance a hannun Atiku da Obi

Gwamna ya yi martani bayan samun 'First Lady' 2 a Osun kan tarbar Remi Tinubu
Gwamna Ademola Adeleke ya magantu kan samun 'First Lady' 2 a Osun kan tarbar Remi Tinubu. Hoto: @AAdeleke_01.
Source: Twitter

Musabbabin samun rudani a Osun

Hakan ya biyo bayan kokarin tarbar Remi Tinubu da matan biyu Titilola Adeleke da Ngozi Adeleke suka yi, cewar The Guardian.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ana sa ran matar shugaban kasar za ta ziyarci birnin Osogbo na jihar a yau Talata 23 ga watan Afrilu.

Sai dai Gwamna Ademola Adeleke ya bayyana cewa Titilola ce za ta tarbi Remi Tinubu a matsayinta na uwargidar jihar.

Martanin Gwamnan Osun kan lamarin

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan, Olawale Rasheed ya fitar a jiya Litinin 22 ga watan Afrilu.

Rasheed ya ce babu wani cece-kuce kan matsayar ofishin uwargidar gwamna a jihar kamar yadda ake yadawa, a cewar Daily Trust.

Ya ce Titilola ita ce uwargida kuma ita ce za ta karbi bakwancin matar shugaban kasa a yau Talata 23 ga watan Afrilu.

Kara karanta wannan

"Musulmi ne ko Kirista": APC da PDP sun gwabza kan ainihin addinin gwamna, an kawo hujjoji

Olawale ya ce sanarwar da aka fitar a baya ba daga ofishin Ngozi Adeleke ya fito ba, inda ya ce an cafke wanda ya haɗa rigimar kuma ya na shan tambayoyi.

APC ta kalubanci Gwamna Adeleke kan addininsa

A wani labarin, kun ji cewa jam'iyyar APC a jihar Osun ta kalubalanci Gwamna Ademola Adeleke kan ainihin addinin da ya ke bi guda daya.

Jam'iyyar ta bayyana haka ne yayin da gwamnan ke ayyana kansa a matsayin Musulmi kuma Kirista a lokaci guda.

A martaninta, jam'iyyar PDP ta ce APC ba ta da manufa shiyasa ta fake da maganar addini domin kawo rudani a jihar Osun.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.