Allahu Akbar: Gwamnan Arewa Ya Ayyana Hutun Kwana 1 a Jiharsa, Ya Kawo Dalili Mai Ƙarfi
- Gwamna Mala Buni ya ayyana hutun kwana ɗaya domin girmama marigayi tsohon gwamnan Yobe, Bukar Abba Ibrahim
- A wata sanarwa da kakakin gwamnan ya fitar, ya ce al'ummar jihar za su yi amfani da ranar domin yi wa marigayin addu'ar uku
- Buni da iyalan marigayin suna zaman makoki da karɓan gaisuwa a gidan gwamnati da ke Damaturu
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Yobe - Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya ayyana ranar Laraba 7 ga watan Fabrairu, 2024, a matsayin ranar hutu domin karrama tsohon gwamnan jihar, Sanata Bukar Abba Ibrahim.
Jaridar The Nation ta tattaro cewa gwamnan ya ba da hutun kwana ɗaya ne a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Yobe, Mamman Mohammed, ya fitar.

Kara karanta wannan
Gwamnan APC ya tono tushen matsalar ƴan bindiga a Arewa, ya jero hanyoyin magance su

Asali: Twitter
Haka nan mutanen Yobe za su kuma yi amfani da wannan rana da babu aiki wajen yin addu'ar uku ga marigayi tsohon gwamnan jihar, Bukar Abba Ibrahim.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Gwamna Buni ya bukaci ‘yan jihar Yobe da su yi amfani da ranar domin yin addu’o’in girmama tsohon shugaban su da Allah ya yi wa rasuwa a kasar Saudiyya.
Idan baku manta ba, Legit Hausa ta kawo muku rahoton cewa tsohon gwamnan jihar Yobe ya rasu ranar Lahadi, 4 ga watan Fabrairu, 2024 a ƙasa mai tsarki.
Za a yi addu'ar uku a gidan gwamnatin jihar Yobe
Sanarwar ta ƙara da bayanin cewa za a gudanar da addu'ar uku ne a masallacin gidan gwamnati da ke Damaturu, babban birnin jihar Yobe a Arewa maso Gabas.
Bayanai sun nuna cewa tun bayan rasuwar tsohon gwamnan, mutane daga ciki da wajen jihar ke zuwa ta'aziyya a gidan gwamnatin, Daily Post ta ruwaito.

Kara karanta wannan
Bidiyon yadda aka binne marigayi tsohon gwamnan Arewa bayan jana'izarsa a masallacin Harami
Gwamna Buni tare da jami’an gwamnati da iyalan marigayin, sun yi ta amsar gaisuwa da ta'aziyyar jama’a a gidan gwamnati da ke Damaturu.
Sanata Bukar Abba Ibrahim, bayan doguwar jinya ya rasu a kasar Saudiyya a ranar Lahadin da ta gabata, inda kuma aka binne shi washe gari.
Gwamnatin Kebbi ta kulle makarantun kuɗi 2
A wani rahoton na daban Wasu manyan makarantun gaba da sakandire na kuɗi sun shiga matsala a jihar Kebbi bisa rashin biyan haƙƙin gwamnati.
Gwamnatin Kebbi karkashin Gwamna Nasir Idris ta sanar da kulle makarantun guda biyu har sai sun biya kuɗaɗen da ake binsu.
Asali: Legit.ng