Kitumurmura Yayin da Majalisa Ta Gayyaci Kwamishinoni 9 da Suka Yi Murabus Don Sake Tantance Su

Kitumurmura Yayin da Majalisa Ta Gayyaci Kwamishinoni 9 da Suka Yi Murabus Don Sake Tantance Su

  • Bayan yin murabus a mukamansu, kwamishinonin jihar Rivers za su dawo kujerunsu yayin da aka yi sulhu
  • Majalisar jihar ta sake gayyatarsu don tantance su da kuma mayar musu da kujerunsu na mukamin kwamishina
  • Wannan na zuwa ne bayan cimma yarjejeniya kan cewa dole a dawo da kwamishinonin mukamansu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Rivers - Majalisar jihar Rivers ta sake gayyatar kwamishinoni tara da suka yi murabus a jihar don tantance su.

Emeka Amadi, Magatakardar Majalisar shi ya bayyana haka a cikin wata sanarwa a yau Litinin 15 ga watan Janairu.

Majalisar jihar PDP ta sake gayyatar kwamishinoni don tantance su
Majalisa Ta Sake Gayyaci Kwamishinoni 9 da Suka Yi Murabus a Rivers. Hoto: Nyesom Ezenwo Wike, Siminalayi Fubara.
Asali: Twitter

Mene dalilin murabus din kwamishinonin?

Idan ba a mantaba a kwanakin baya kwamishinoni da dama sun yi murabus daga mukaminsu a gwamnatin Siminalayi Fubara.

Kara karanta wannan

Bayan nasara a Kotun Koli, Gwamna Abba Gida-Gida ya ba Kwankwaso, Ganduje da Gawuna mukamai

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Murabus din nasu na da alaka da rashin jituwa tsakanin gwamnan da mai gidansa, Nyesom Wike a jihar, cewar Channels TV.

Sai dai a cikin sharudan zaman lafiya da aka kulla wanda Shugaba Tinubu ya jagoranta akwai dawo da kwamishinonin mukaminsu a jihar.

Majalisar karkashin jagorancin Hon. Hon Martin Amaewhule ta gayyace su ne don mayar musu da kujerunsu bayan tantance su.

Yaushe za a sake tantance kwamishinonin?

Sanarwar ta ce:

"Majalisar jihar Rivers ta na gayyatar wadannan kwamishinoni don tantance su a matsayinsu na mambobin zartarwa a jihar."

Kwamishinonin sun hada da:

1. Zacchaeus Adangor SAN

2. ⁠Dakta Jacobson Mbina

3. ⁠Dakta Gift Worlu

4. Inime Chinwenwo- Aguma

5. ⁠Injiniya Chukwuemeka Woke

6. ⁠Farfesa Prince Chinedu Mmom

7. ⁠Dakta George-Kelly D. Alabo

8. ⁠Hon. Isaac Kamalu

9. ⁠Injiniya Austin Ben Chioma.

Kara karanta wannan

Bayan dakatar da N-Power, Tinubu ya dauki matakin karshe kan shirin NSIPA, ya fadi dalili

Za a gabatar da tantancewar a ranar Laraba 17 ga watan Janairu a misalin karfe 10 na safe a harabar Majalisar da ke Port Harcourt, cewar Leadership.

Har ila yau, sanarwar ta bukaci wadanda za a tantance din su zo da takardunsu don binciken kwa-kwaf.

Wike ya tura sako ga Fubara kan 2027

A wani labarin, Ministan Abuja, Nyesom Wike ya sake caccakar Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Rivers.

Wike ya ce ya kamata a bari sai zaben 2027 ya zo a nan za a gane waye ne sama da wani a tsakaninsu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.