Zan Nuna Maka Ni Waye, Ministan Tinubu Ya Dira Kan Yaron Gidansa, Ya Gargade Shi Kan Zaben 2027

Zan Nuna Maka Ni Waye, Ministan Tinubu Ya Dira Kan Yaron Gidansa, Ya Gargade Shi Kan Zaben 2027

  • Rikici ya kara dagule wa bayan Ministan Abuja, Nyesom Wike ya tura zazzafan gargadi ga yaron gidansa, Siminalayi Fubara
  • Wike ya ce a yanzu ba lokacin siyasa ba ne amma idan lokacin ya zo za a gane waye ne a saman wani
  • Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da takun saka tsakanin Gwamna Fubara da mai gidansa, Nyesom Wike

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Ministan Abuja, Nyesom Wike ya tura sakon gargadi ga Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Rivers.

Wike ya bayyana cewa a yanzu ba lokacin siyasa ba ne amma idan lokacin ya yi za a gane waye ne a sama.

Kara karanta wannan

Mun gaji: Ba za mu lamunci sace mana ‘ya’ya da sayar da su ba, Sarkin Kano ya fusata

Wike ya gargadi Gwamna Fubara kan zaben 2027 mai zuwa
Wike ya yi alwashin fito wa da karfi a zaben 2027. Hoto: Nyesom Wike, Siminalayi Fubara.
Asali: Facebook

Mene Wike ke cewa ga Fubara?

Ministan ya bayyana haka ne a yau Asabar 6 ga watan Disamba yayin ganawa da tsohon amininsa a siyasa, Cif Victor Giadom.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce bai damu da dukkan zage-zagen da ake yi a kafofin yada labarai ba inda ya ce ba a zabe a kafar sadarwa, cewar Vanguard.

Ya kara da cewa lokacin zabe zuwa suka yi suka roki jama'a kuma suka amince dasu don haka ba a siyasa a kafafen sadarwa.

Wane gargadi Wike ya tura ga Fubara?

Ya ce:

"Yanzu ba lokacin siyasa ba ne, idan lokacin ya yi a nan za a gane waye a gaba.
"Idan kaga dama ka yi ta zagi na yadda kake so, ko ka dauko wasu a kafafen sadarwa su zage ni ban damu ba.
"Amma lokacin siyasa na zuwa, ba mu tsaya takara a kafafen sadarwa ba, mun yi wa mutane magana kuma sun amince da mu."

Kara karanta wannan

Ku sake ba ni dama: Tsohon gwamnan Arewa ya fadi darussan da ya koya a gidan kaso, ya tura bukata

Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da takun saka tsakanin Gwamna Fubara da mai gidansa, Nyesom Wike, cewar Channels TV.

An rushe Majalisar jihar Rivers

A wani labarin, Yayin da rikicin siyasa ke kara kamari a jihar Rivers, Gwamna Siminalayi Fubara ya umarci rushe Majalisar jihar.

Wannan na zuwa ne yayin ake ci gaba da takun saka tsakanin Gwamna Fubara da Nyesom Wike.

Daga bisani Shugaba Tinubu ya nuna rashin jin dadinsa kan rushe Majalisar inda ya ce ita ce martabar dimukradiyya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.