Rashin Fahimtar Turanci Ke Sa Cewa Akwai Kuskure a CTC, Kperogi Ya Zargi Alakai Kan Hukuncin Kano

Rashin Fahimtar Turanci Ke Sa Cewa Akwai Kuskure a CTC, Kperogi Ya Zargi Alakai Kan Hukuncin Kano

  • Yayin da ake ci gaba da tofa albarkacin baki kan fitar da takardun CTC, Farfesa Farouk Kperogi ya yi martani kan matsalar
  • Kperogi ya ce wadanda ba sa fahimtar Turanci ne kawai za su kira hakan da kuskure a ciki daman haka hukuncin ta ke
  • Farfesan ya ce ya tabbata alkalan kotun sun yi hukunci ne ba tare da duba hukuncin karamar kotun ba a baya

Abdullahi Abubakar, kwararren editan siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano – Farfesa Farouk Kperogi ya yi martani kan fitar da takardun CTC da kotun daukaka kara ta yi a Kano.

Kperogi ya ce babu wata maganar kuskure a cikin takardun CTC da kotun ta fitar da ya jawo cece-kuce, Legit ta tattaro.

Kara karanta wannan

Shari’ar Kano: Gwamna Abba ba zai maida takardun hukuncin kotu ba Inji Lauyan NNPP

Kperogi ya yi martani kan kuskuren takardun CTC a jihar Kano
Kperogi ya zargi alkalan kotu kan hukuncin zaben Kano. Hoto: Abba Kabir, Nasiru Gawuna.
Asali: Facebook

Mene Kperogi ke cewa kan hukuncin Kano?

Farfesan ya ce ya tabbata alkalan kotun sun yi hukunci ne ba tare da duba hukuncin karamar kotun ba a baya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce daga bisani an samu wasu abubuwa da su ka sha bam-ban da hukuncin wanda hakan ya tilasta su sake rubuta hukuncin nasu.

Ya ce:

“A yayin sake rubuta hukuncin nasu, sun yi fatali da hukuncin karamar kotun a baya wanda hakan ya jawo cece-kuce."

Kperogi ya bayyana ma'anar kuskure

Ya kara da cewa:

“Wannan kuskure da su ke magana ba komai ba ne illa burbudin kura-kurai a baya, wadanda ba sa fahimtar Turanci ne za su kira hakan kuskure.”

Kperogi ya ce ta yaya za a ce wai takardun CTC an yi kuskure a ciki, ba zai yiwu ace dukkan abin da aka rubuta kuskure ba ne.

Kara karanta wannan

Kano: Alkalai 'yan Adam ne ba ma'asumai ba, APC ta fadi yadda za a gyara bayan fitar CTC

Ya ce abin da ake kira da kuskure shi ne rubuta wani abu ko harafi wanda hakan ba zai sauya komai a shari’ar ba.

Yan sanda sun gargadi APC, NNPP kan zanga-zanga

A wani labarin, rundunar ‘yan sanda a jihar Kano ta gargadi magoyan bayan jam’iyyun APC, NNPP kan gudanar da zanga-zanga a jihar.

Wannan na zuwa ne yayin da ake shirin yin zanga-zanga bayan fitar da takardun CTC da su ka jawo cece-kuce.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.