PDP Ta Kara Shiga Matsala Yayin da Kotun Daukaka Kara Ta Tsige Yan Majalisa 11 a Jihar Filato
- Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta kori ‘yan majalisa 11 na jam’iyyar PDP a Filato
- Kotun daukaka kara ta kori yan majalisar PDP 11 a majalisar dokokin jihar Filato a ranar Juma’a, 24 ga watan Nuwamba
- Kwamitin da Mai Shari’a Okon Abang ya jagoranta ya yanke hukuncin cewa PDP ba za ta iya daukar nauyin ‘yan takara a zaben da ya gabata
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum
Jihar Plateau - Kotun daukaka kara da ke zama a Abuja, ta tsige yan majalisa 11 na jam'iyyar PDP a majalisar dokokin jihar Filato a ranar Juma'a, 24 ga watan Nuwamba.
A wani hukunci na bai daya, kwamitin kotun karkashin jagorancin Mai shari'a Okon Abang, ya tabbatar da cewar dukkan yan majalisar da aka tsige sun samu kuri'u marasa amfani a zabenna watan Maris saboda jam'iyyarsu bata da tsari, jaridar Daily Trust ta rahoto.

Kara karanta wannan
Jerin abubuwa 2 muhimmai da ya kamata ku sani yayin da ake yanke hukuncin shari'ar zaben Nasarawa

Asali: Facebook
Ya kara da cewar jam'iyyar PDP ta saba sashi na 177 na kundin tsarin mulkin 1999, saboda haka ba za ta iya daukar nauyin yan takara a zabe ba.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Saboda haka, kotun ta ayyana dukkanin wadanda suka zo na biyu a zaben na ranar 18 ga watan Maris a matsayin wadanda suka lashe zabe.
Jerin yan majalisar da kotu ta tsige
- Hon Timothy Dantong (Riyom)
- Hon. Rimyat Nanbol,- (Langtang ta Arewa ta Tsakiya)
- Moses Sule (Mikang)
- Salome Waklek,-(Pankshin)
- Hon. Bala Fwangji (Mangu ta Kudu)
- Hon. Maren Ishaku (Bokkos)
- Hon. Dagogot (Quaanpan ta Arewa)
- Hon Nannim Langyi,-(Langtang ta Arewa maso Arewa)
- Hon Nimchak Rims (Langtang ta Kudu)
- Hon. Danjuma Azi (Jos ta Arewa maso Yamma)
- Hon Gwottson Fom (Jos ta Kudu)
- Hon. Abubakar Sani idris (Mangu ta Arewa)

Kara karanta wannan
NNPP ta aika sako ga NJC kan hukuncin kotun daukaka kara na korar Gwamna Abba na Kano
A yanzu jam'iyyar All Progressives Congress (APC) ce jam'iyya mai jagoranci a majalisar.
Kotu ta tabbatar da zaben Nasir Idris
A gefe guda, Legit Hausa ta rahoto a baya cewa kotun daukaka kara da ke zama a Abuja, ta tabbatar da nasarar Nasir Idris a matsayin sahihin zababben gwamnan jihar Kebbi a zaben ranar 18, ga watan Maris.
Kwamitin kotun mai mutum uku, ya bayyana a ranar Juma'a, 24 ga watan Nuwamba, cewa karar da jam'iyyar PDP da dan takararta na zaben gwamnan, Janar Aminu Bandel bai da inganci, jaridar Daily Trust ta rahoto.
Asali: Legit.ng