Kano: Sabon Rikici Ya Barke a Kotu Tsakanin Lauyoyin Abba da Alkalan Kotu Kan Fitar da Takardun CTC

Kano: Sabon Rikici Ya Barke a Kotu Tsakanin Lauyoyin Abba da Alkalan Kotu Kan Fitar da Takardun CTC

  • An kaure a kotun daukaka kara tsakanin lauyoyin Abba Kabir da alkalan kotun kan fitar da takardun CTC da ke nuna nasarar Abba
  • Lauyoyin gwamnan sun isa kotun ne don daukaka kara inda su ka nemi a sauya hukuncin da ya ba su rashin nasara
  • Wannan na zuwa ne bayan fitar da takardun CTC da kotun ta yi wanda ke nuna cewa Abba Kabir ne ya yi nasara a shari'ar zaben

Abdullahi Abubakar, kwararren editan siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano – Rikici ya sake barkewa yayin da lauyoyin Gwamna Abba Kabir suka je daukaka kara a kotu.

Layoyin gwamnan sun samu wata ‘yar hatsaniya da alkalan kotun bayan fitar da takardun CTC da ke tabbatar da nasarar Abba Kabir, Legit ta tattaro.

Kara karanta wannan

Kungiyar Arewa ta bayyana hukuncin da ya kamata Kotun Koli ta yanke a shari'ar jihar Kano

Rikici ya kaure tsakanin lauyoyin Gwamna Abba Kabir da alkalan kotun daukaka kara
Sabon rikici ya barke tsakanin lauyoyin Abba da alkalan kotu. Hoto: Court of Appeal.
Asali: Facebook

Mene ya jawo sabon rikicin?

Sabon rikicin ya barke ne bayan dukkan bangarorin sun ki amincewa da juna kan takardun CTC da kotun ta fitar a jiya, cewar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Lauyoyin Gwamna Abba Kabir sun kai korafi na daukaka kara a Abuja inda su ke neman adalci a hukunci da aka yi a kuskure.

Har ila yau, alkalan kotun daukaka karar sun ki amincewa da bukatarsu a kotun inda hakan ya tilasta lauyoyin zuwa kotun shiyya da ke Kano.

Har ila yau, alkalan kotun sun tura takarda ga lauyoyin don gyaran kura-kurai a takardun CTC wanda lauyoyin Abba Kabir su ka ki.

Wane hukunci kotun ta yanke?

A ranar Juma'a ce 17 ga watan Nuwamba gamayyar alkalan guda uku su ka sake rusa zaben Gwamna Abba Kabir na jihar Kano.

Kara karanta wannan

Abba Vs Gawuna: 'Yan sanda sun roki malaman addini su dage da yin wa'azi kan tada tarzoma a Kano

Kotun karkashin jagorancin Mai Shari'a, Moore Adumein ta rusa zaben kan zargin cewa Gwamna Abba Kabir na jihar Kano ba dan jam'iyyar NNPP ba ne.

Amma a takardun CTC, kotun ta yi watsi da hukuncin karamar kotun inda ta umarci biyan Abba Kabir naira miliyan daya.

Jam'iyyar NNPP ta yi martani kan takardun CTC

A wani labarin, Jami'yyar NNPP ta yi martani kan shari'ar zaben gwamnan Kano bayan fitar da takardun CTC.

NNPP ta ce abin takaici ne yadda Najeriya ta zubar da mutuncinta musamman a bangaren shari'a.

Ta yi zargin da nufi aka yi saboda rashin fitar da takardun da wuri ganin cewa mai daukaka kara ya na kwanaki 14 ne kacal.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.