Kotun Ɗaukaka Kara Ta Tanadi Hukunci Kan Nasarar Gwamnan APC na Arewa da aka tsige

Kotun Ɗaukaka Kara Ta Tanadi Hukunci Kan Nasarar Gwamnan APC na Arewa da aka tsige

  • Kotun ɗaukaka kara ta shirya, ta tanadi hukunci domin raba gardama kan sahihin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Nasarawa
  • A baya Kotun zaɓe ta tsige Gwamna Abdullahi Sule na APC, ta ayyana ɗan takarar PDP a matsayin zababben Gwamna
  • Sai dai Gwamna Sule ya garzaya Kotun ya ɗaukaka kara kuma Alƙali ya ce za a sa ranar yanke hukunci nan gaba kaɗan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, gogaggen Edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Kotun ɗaukaka ƙara mai zama a Abuja ta tanadi hukuncinta kan ƙarar da Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, na APC ya shigar gabanta.

Kotun ɗaukaka kara zata raba gardama kan zaben Gwamnan Nasarawa.
Kotun Daukaka Kara Ta Tanadi Hukunci Kan Zaben Gwamnan Jihar Nasarawa Hoto: Abdullahi Sule, David Ombugadu
Asali: Facebook

Gwamnan ya ɗaukaka ƙara zuwa Kotun ɗaukaka ƙara yana kalubalantar mafi akasarin hukuncin Kotun zabe, wadda ta tsige shi daga matsayin Gwamnan Nasarawa.

Kara karanta wannan

Zanga-zanga ta ɓarke bayan Kotun ɗaukaka ƙara ta tsige yan majalisar tarayya 4 na PDP a jihar arewa

Kotun sauraron ƙorafe-korafen zaɓen Gwamnan Nasarawa ta sauke Sule kana da ayyana ɗan takarar PDP, David Ombugadu a matsayin wanda ya lashe zaɓe, The Nation ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kotun ɗaukaka kara zata raba gardama

Yayin zaman sauraron ƙarar da Gwamna Sule ya ɗaukaka, kwamitin alkalai uku na Kotun ɗaukaka ƙara karkashin mai shari'a Uchechukwu Onyemenam, ya ce za a sanar da ranar yanke hukunci.

Alƙalin ya shaida wa kowane ɓangare da ƙarar ta shafa cewa nan bada daɗewa ba Kotun zata faɗi ranar yanke hukunci kan sahihin wanda ya ci zaɓen Nasarawa.

Yadda zaman Kotun ya kasance

Yayin zaman sauraron ƙarar, Lauyan Gwamna Sule, Wole Olanipekun, ya roƙi Kotun ɗaukaka ƙara ta rushe hukuncin Kotun zaɓe, Channels tv ta ruwaito.

Olanipekun ya shaida wa Alƙalan cewa Kotun zaɓe ta musu rashin adalici yayin da ta ƙi karban bayanan shaidun da suka gabatar kuma ta yi watsi da alƙaluman BVAS da aka miƙa mata.

Kara karanta wannan

Hadimin Shugaba Tinubu ya magantu kan zaben Bayelsa, ya aike da sako ga gwamna Diri na PDP

Bayan gama bayanansa, lauyan PDP da ɗan takararta Ombugadu, Kanu Agabi, ya roƙi Kotun ta kori ƙarar da aka ɗaukaka wacce ta kalubalanci hukuncin Kotun zaɓe.

Agabi, wanda ya kafa hujja da hukuncin da kotun zaɓe ta yanke, ya ce a yayin da take yanke hukunci, karamar kotun ta yi cikakken bayani kan yadda ta cimma wannan matsaya.

Kotu zata yanke hukunci kan zaben Legas

A wani labarin na daban kuma Kotun daukaka kara ta fara zaman sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Lagas na 2023.

A yau laraba, 15 ga watan Nuwamba, ne kotun za ta yanke hukunci a kan shari'ar da ke neman a tsige Babajide Sanwo-Olu daga kujerar gwamnan Lagas.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262