Rigima ba ta Kare ba, NNPP da Kwankwaso Za Su Gwabza a Kan Tambarin Jam’iyya
- Wasu jagororin NNPP sun nuna babu ruwansu da kokarin da ake yi a canza tambarin jam’iyya
- Rabiu Musa Kwankwaso da mutanensa su na shirin kawo canza a kundin tsarin mulkin NNPP
- Peter Ogah ya sanar da hukumar INEC cewa wadanda su ka kafa jam’iyya ba su san da batun ba
Abuja - Jam’iyyar NNPP ta rubutawa hukumar INEC takarda a game da shirin da wasu su ke yi na canza tambarin da aka san ta da shi.
Vanguard ta kawo rahoto dazu cewa Peter Ogah ya rubuta wasika a madadin jam’iyyar wanda ta shiga hannun manema labarai a Legas.
Haka kuma jam’iyyar adawar ta kuma aika takarda zuwa ga Rabiu Musa Kwankwaso domin a janye yarjejeniyar da aka yi da Kwankwasiyya.

Asali: Twitter
Hukumar dillacin labarai na kasa ta ce Mista Peter Ogah ya zargi wasu marasa hurumi da neman canza masu tambari da tsarin mulki.
Kwankwaso ba su da hurumi a NNPP?
"Mu ne lauyoyin jam’iyyar NNPP, ta karkashin Dr Boniface Okechukwu Aniebonam wanda ya kafa ta da shugaban BOT, Dr Temitope Aluko, mu na rubuto wannan bisa umarninsu
Wadanda mu ke karewa a gaban shari’a sun ce wasu daidaikun mutane su na yunkurin canza tambarin jam’iyya kuma su canza doka, saboda haka dole mu fito da wannan sanarwa.
Ana sanar da hukumar a doka cewa wasu da ba su da iko su na wannan mugun tsari, saboda haka dole ayi watsi da wannan ko kuma ka da a saurari wanin canji da bai fito daga jam’iyya ba."
- Peter Ogah
The Nation ta ce Ogah a wasikarsa ya yi godiya ga hukumar INEC bisa bin dokar kasa da ta ke yi.
Yarjejeniyar Kwankwasiyya da NNPP
A game da ‘dan takaran shugaban kasa na 2023, takardar ta tuna masa yarjejeniyar da aka yi a Fabrairun 2022 tsakanin Kwankwasiyya da NNPP.
A cewar Ogah, jagororin NNPP sun godewa mabiya Kwankwasiyya da su ka hada-kai da su a zaben 2023, su ka ce yanzu Allah ya raka taki gona.
Yadda za a gyara zaben Najeriya
A ra’ayin Osita Chidoka, an ji ya na cewa bai dace a rika shari’ar sauraron karar zabe bayan an yi rantsuwa ba saboda ba za ayi adalci a kotu ba.
‘Dan siyasar ya na so a wajabta samun goyon bayan 50% a zabe kafin ‘dan takara ya karbi mulki, hakan zai kara farin jini da karbuwar shugaba.
Asali: Legit.ng