Tinubu Zai Halarci Taron G20 Da Zai Gudana a New Delhi Na Kasar Indiya

Tinubu Zai Halarci Taron G20 Da Zai Gudana a New Delhi Na Kasar Indiya

  • Shugaba Bola Tinubu zai shilla zuwa Indiya domin taron halartar taron ƙasashen G20
  • Taron zai gudana ne a ranar tara da kuma 10 ga watan Satumban nan da muke ciki
  • Za a tattauna muhimman abubuwa da za su kawowa Najeriya ci gaba a yayin gudanar da taron

FCT, Abuja - Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, zai tafi zuwa birnin New Delhi na ƙasar Indiya domin halartar taron ƙasashe masu ƙarfin tattalin arziƙi na G20.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Cif Ajuri Ngelale ne ya bayyana hakan a yayin da yake zantawa da manema labarai a gidan gwamnati.

Tinubu zai lula zuwa ƙasar Indiya
Shugaba Tinubu zai halarci taron G20 da zai wakana a ƙasar Indiya. Hoto: Daily Trust
Asali: UGC

Me zai kai Tinubu wajen taron na G20 na bana?

Taron G20 na bana dai zai gudana ne a New Delhi, babban birnin ƙasar Indiya a ranakun tara da 10 ga watan Satumban nan da muke ciki kamar yadda Daily Trust ta wallafa.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu Ya Gana da Tsohon Gwamnan Jihar Arewa a Aso Villa, Sahihan Bayanai Sun Fito

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Ajuri ya bayyana cewa a yayin taron, Shugaba Bola Tinubu zai haɗu da takwarorinsa shugabannin ƙasashe daga sassa daban-daban na duniya.

Ya ƙara da cewa Tinubu zai gabatar da jawabi a gaban shugabannin duniya da kuma manyan 'yan kasuwa masu zuba hannayen jari.

Amfanin taron na G20 ga Najeriya

Ajuri Ngelale ya ƙara da cewa a yayin taron Shugaba Tinubu zai gana da takwaransa na Brazil, Firaministan Indiya, shugaban ƙasar Koriya ta Kudu da shugaban gwamnatin Jamus.

Ya kuma ce Tinubu zai gana da shugabannin manyan kamfanoni na duniya, inda ake sa ran zai janyo wasu daga cikinsu domin su zo su zuba hannayen jari a Najeriya.

Ngelale ya kuma tabbatar da cewa shugaban zai yi amfani da wannan dama ta halartar taron wajen ganin an kawowa Najeriya wani abu na ci gaban 'yan ƙasa kamar yadda New Telegraph ta wallafa.

Kara karanta wannan

An Bayyana Babban Abu 1 Da Ya Jawo Ƙaruwar Juyin Mulkin Sojoji a Nahiyar Afirka

Ƙasashen na G20 dai su ne; Argentina, Australia, Brazil, Canada, China, Faransa, Jamus, Indiya, Indonesia, Italiya, Japan, Koriya ta Kudu, Mexico, Rasha, Saudi Arabia, Afrika ta Kudu, Turkiya, Ingila, da Amurka, sai kuma tarayyar Turai (EU).

Wike ya ce Tinubu yake yi wa aiki ba APC ba

Legit.ng a baya ta yi rahoto kan iƙirarin da ministan birnin tarayya Nyesom Wike ya yi na cewa Shugaba Tinubu yake yi wa aiki ba jam'iyyar APC mai mulki ba.

Wike ya kuma jaddada cewa har yanzu yana nan a cikin jam'iyyarsa ta PDP babu wanda ya isa ya dakatar da shi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Deen Dabai avatar

Deen Dabai Zaharaddeen Hamisu marubuci kuma ma'aikacin jarida ne da ke da gogewa wajen iya tantance sahihan labarai da na karya. Ya yi digirinsa a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Baya ga haka, ya shafe sama da shekaru 5 a bangaren aikin watsa labarai wanda hakan ya bashi gogewa ta musamman a aikin jarida. Za a iya tuntubarsa ta adireshinsa na yanar gizo: deen.dabai@corp.legit.ng