Shugaba Tinubu Ya Ce Sojojin Gabon Sun Tabbatar Ma Sa Da Abinda Yake Fargaba Game Da Nijar

Shugaba Tinubu Ya Ce Sojojin Gabon Sun Tabbatar Ma Sa Da Abinda Yake Fargaba Game Da Nijar

  • Shugaba Bola Tinubu ya bayyana cewa abinda yake tsoro ne ya faru a ƙasar Gabon
  • Ya ce ya hasaso cewa sojojin wasu ƙasashen za su yi ƙoƙarin kwaikwayon abinda sojin Nijar suka yi
  • Ya bayyana hakan ne a yayin da ya karɓi baƙuncin tawagar sarkin Musulmi, Muhammad Sa'ad Abubakar III a Abuja

FCT, Abuja - Shugaba Bola Tinubu ya bayyana cewa abinda yake gujewa bayan juyin mulkin da aka yi a Nijar, ya tabbata a juyin mulkin da sojoji suka yi wa Ali Bongo na Gabon.

Ya bayyana hakan ne ranar Alhamis, a lokacin da ya karbi baƙuncin Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya, ƙarƙashin jagorancin mai alfarma Sarkin Musulmi, Muhammadu Sa'ad Abubakar III.

Tinubu ya ce abinda yake fargaba ya tabbata
Shugaba Tinubu ya ce sojojin Gabon sun tabbatar da abinda yake fargaba. Hoto: @officialABAT, @HQNigerianArmy
Asali: Twitter

Sojojin Gabon sun tabbatar da abinda Tinubu yake fargaba

Kara karanta wannan

An Bayyana Babban Abu 1 Da Ya Jawo Ƙaruwar Juyin Mulkin Sojoji a Nahiyar Afirka

Tinubu ya bayyana cewa za su yi duk mai yiwuwa wajen ganin sun kawo ƙarshen rikicin Nijar ta hanyoyi na diflomasiyya, kafin a kai ga zuwa yaƙi, wato mataki na ƙarshe da za a iya ɗauka.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu ya jaddada cewa duk wani nau'i na ƙwatar mulki da sojoji suke yi daga hannun farar hula, abin a yi Allah wadai ne da shi kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Tinubu ya ƙara da cewa juyin mulkin da aka gudanar a ƙasar Gabon ya tabbatar da abinda yake tsoro na cewar sojojin wasu ƙasashen za su kwaikwayi abinda aka yi a Nijar.

Da safiyar ranar Laraba, 30 ga watan Agusta ne aka wayi gari da juyin mulkin da sojoji suka yi wa Ali Bongo na ƙasar Gabon.

Tinubu ya ce Najeriya ba ta son yakar Nijar

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu Ya Maida Martani Kan Sabon Juyin Mulkin da Sojoji Suka Yi a Gabon, Ya Faɗi Mataki Na Gaba

Tinubu ya godewa Sarkin Musulmi bisa ziyarce-ziyarcen da suka kai jamhuriyar Nijar, inda ya shaida ma sa cewa za su ƙara komawa domin a kawo ƙarshen rikicin.

Ya ce Najeriya ba za ta yaƙi jamhuriyar Nijar ba kasantuwarta maƙwabciyarta, wacce kuma take da alaƙa ta ɓangarori da dama da ita kamar yadda Nigerian Tribune ta wallafa.

Ya ƙara da cewa kowa na ganin abinda yaƙi ya janyo a Ukraine da kuma Sudan, sai dai ya ce hakan ba yana nufin za a zura ido a bar abinda ya faru a Nijar ɗin ya ci gaba da faruwa ba.

Tinubu ya kuma bayyana cewa suna sane da halin da 'yan Nijar suke ciki, a dalilin hakan ne suke son sojojin su yi abinda ya kamata domin a cirewa ƙasar takunkuman da aka sanya ma ta.

Tinubu ya yi martani kan juyin mulkin Gabon

Legit.ng a baya ta yi rahoto kan Allah wadai da juyin mulkin da sojoji suka yi a ƙasar Gabon da Tinubu ya yi.

Kara karanta wannan

Sojojin Juyin Mulkin Gabon Sun Zayyano Dalilai 4 Da Suka Sanyasu Kifar Da Gwamnatin Kasar

Tinubu ya ce ba za su lamunci abinda ke faruwa a ƙasashen Afrika ba, kuma za su yi aiki tare da kungiyar Tarayyar Afrika don ganin an ɗauki mataki a kan Gabon.

Asali: Legit.ng

Authors:
Deen Dabai avatar

Deen Dabai Zaharaddeen Hamisu marubuci kuma ma'aikacin jarida ne da ke da gogewa wajen iya tantance sahihan labarai da na karya. Ya yi digirinsa a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Baya ga haka, ya shafe sama da shekaru 5 a bangaren aikin watsa labarai wanda hakan ya bashi gogewa ta musamman a aikin jarida. Za a iya tuntubarsa ta adireshinsa na yanar gizo: deen.dabai@corp.legit.ng