Ganduje: Abin da Ke Jawo Mataimakan Gwamnonin Jihohi Su Yi Fada da Gwamnoni

Ganduje: Abin da Ke Jawo Mataimakan Gwamnonin Jihohi Su Yi Fada da Gwamnoni

  • Abdullahi Umar Ganduje ya karbi bakuncin tsofaffin Gwamnonin jihohi a sakatariyar jam’iyyar APC
  • Shugaban APC ya yi magana game da alakar Gwamnonin da Mataimakansa da abin ke jawo rigingumu
  • Ganduje wanda ya san gwamnati da kyau, ya ce dokar kasa ba ta yankewa Mataimaki wani aiki ba

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Abuja - Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje ya yi magana game da alakar gwamnonin jihohi da mataimakin gwamnonin jihohi.

The Guardian ta ce Dr. Abdullahi Umar Ganduje wanda ya hadu da tsofaffin Gwamnonin jihohi, ya fadi abin da ke jawo rikici a gidajen gwamnatoci.

Shugaban jam’iyyar APC na kasan ya zargi ‘yan kanzagi da hura wutar rikicin siyasar da ake samu, yanzu haka gwamnatin NNPP ta na bincikensa a Kano.

Abdullahi Ganduje da mataimakinsa
Shugaban APC da mataimakinsa a Kano Hoto: Abdullahi Umar Ganduje OFR
Asali: Facebook

Mataimakan gwamnoni ba banza ba

Kara karanta wannan

Dalilin Da Yasa Ba a Taba Jin Kaina Da Bagudu Ba, Tsohon Mataimakin Gwamnan Kebbi Ya Magantu

‘Dan siyasar ya ke cewa bai kamata a rika raina mataimakan gwamnoni ba domin amfaninsu ya na tashi a duk lokacin da gwamna ya shiga wata larura.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Tun da kundin tsarin mulkin kasa bai yi bayanin nauyin da ke kan wuyan mataimaki ba, shi kan shi Ganduje ya misalta su da tayar faci a mota.

Ko da direba bai bukatar tayan a lokacin da abubuwa su ke tafiya kalau a mota, ya ce da zarar ya shiga matsala zai fara neman inda karamar tayar ta shiga.

Dr. Ganduje ya rubuta littafi

Ko a yanzu haka ana samun matsala tsakanin wani gwamna da mataimakin shi, saboda shawo kan irin haka ‘dan siyasar ya rubuta littafi a kan batun.

P/Times ta ce tsohon Gwamnan na jihar Kano ya rubuta littafi mai suna “Deputising and Governance in Nigeria” da ya shafi mulki da taimakawa masu iko.

Kara karanta wannan

Tinubu Ya Dauko Tsofaffin Gwamnonin Arewa 2, Ya Ba Su Aikin Nade-Nade a Gwamnati

"Idan ka na mataimaki, sai ka tsaya gefen gwamna domin ka saurare shi da kyau kuma shi ma ya saurare ka, za a ce ai shirme kurum ka ke fada.
Idan ka shiga gaba domin bada kariya ko da an samu hadari ko miyagun abubuwa kamar macizai su fado, ‘yan kanzagi za su ce ka sha gaban shi.
Idan ka girmama mai gidanka, ka tsaya a bayan shi, ‘yan kanzagi za su ce ka na sanya, ka yi watsi da shi, to yanzu wani matsayi za ka dauka?"

- Abdullahi Umar Ganduje

Ganduje a gidan gwamnatin Kano

Ganduje wanda ya yi aiki da Rabiu Musa Kwankwaso na tsawon shekaru takwas, ya ce bai bari irin wadannan mutane sun hada shi fada a mulki ba.

Har Rabiu Kwankwaso ya kammala mulki, ya mikawa Ganduje ba a taba jin wani sabani a tsakaninsu ba, duk da dai Hafizu Abubakar ya bar shi.

A 2018 Farfesa Hafiz Abubakar lokacin ya na Mataimakin gwamnan jihar Kano ya ce Ganduje ya na azabtar da shi, daga baya ya sauka daga kujerarsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng