Daga karshe, Ganduje ya nada Gawuna matsayin mataimakin gwamna

Daga karshe, Ganduje ya nada Gawuna matsayin mataimakin gwamna

Jaridar Daily Nigerian ta samu rahoton cewa gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya zabi kwamishanan aikin noma, Nasiru Gawuna, a matsayin mataimakin gwamnan jihar.

Kimanin wata daya kenan da Ganduje ke shugabancin jihar ba tare da mataimaki ba tun lokacin da tsohon mataimakin farfesa Hafiz Abubakar yayi murabus ranan 5 ga watan Agusta.

An zabi Malam Nasiru Gawuna wanda tsohon shugaban karamar hukuma ne kuma shugaban kungiyar wasannin matasan Najeriya cikin mutani hudu da gwamnan ke kokarin zaba.

Daga karshe, Ganduje ya nada Gawuna matsayin mataimakin gwamna
Daga karshe, Ganduje ya nada Gawuna matsayin mataimakin gwamna
Asali: Facebook

KU KARANTA: Cikakken tarihin Bajimin Malamin Musulunci Imam Bukhari

Majiyar tace: "An rigaya da tura sunansa majalisar dokokin jihar domin bincike. Ana sa ran rantsar da shi ranan Talata ko Laraba ,"

Gabanin haka, gwamna Ganduje ya mika sunan Nasiru Gawuna a matsayin wanda zai tsaya takara da shi a matsayin mataimakin gwamna a 2019.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel