Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Amince da Nadin Kwamishinoni 18

Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Amince da Nadin Kwamishinoni 18

  • Majalisar dokokin jihar Zamfara ta tantance tare da tabbatar da naɗin sabbin kwamishinoni 18 da gwamna Dauda Lawal ya aiko mata
  • Mambobin majalisar sun yi aikin tantance mutanen ne a zamansu na ranar Alhamis, 3 ga watan Agusta, 2023
  • Tun da farko gwamna Dauda Lawal ya aike da sunayen mutum 18 ga majalisar domin tantance su

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Zamfara State - Majalisar dokokin jihar Zamfara ta tantance tare da tabbatar da naɗin mutane 18 da Gwamna Dauda Lawal ya aika mata a matsayin kwamishinoni.

Jaridar Vangaurd ta tattaro vewa hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na majalisar, Malam Nasiru Biyabiki ya fitar a Gusau ranar Alhamis.

Zauren majalisar dokokin jihar Zamfara.
Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Amince da Nadin Kwamishinoni 18 Hoto: vanguard
Asali: UGC

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa a kwanakin baya ne majalisar dokokin jihar ta 7 ta sanar da karbar mutane 18 da Lawal ya naɗa a kwamishinoni.

Kara karanta wannan

Gwamna Radda Ya Rantsar da Sabbin Kwamishinoni 20 da Hadimai 18, Ya Raba Ma'aikatar Ilimi Gida Biyu

Kakakin majalisar dokokin ya ce:

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

“An tantance wadanda gwamna ya nada kuma an tabbatar dasu a zauren majalisar da ke Gusau ranar Alhamis, 3 ga watan Agusta, 2023."

Jerin sunayen sabbin kwamishinonin da majalisar da tabbatar

Nasiru Buyabiki ya bayyana sunayen sabbin kwamishinonin da majalisar da amince da naɗinsu ranar Alhamis, ga su kamar haka;

1. Sule Adamu

2. Salisu Musa

3. Kabiru Birnin-Magaji

4. Yau Haruna-Bakura

5. Abdurrahman Tumbido

6. Lawali Barau

7. Nasiru Ibrahim

8. Tasiu Musa

9. Mannir Haidara

10. Kyaftin Bala Mairiga mai ritaya

11. Abdul’aziz Sani (SAN)

12. Ahmed Yandi

13. Wadatau Madawaki

14. Aisha Anka

15. Bello Auta

16. Abdulmalik Gajam

17. Mahmud Muhammad

18. Dakta Nafisa Maradun.

Tun da farko, shugaban masu rinjaye na majalisar, Malam Bello Mazawaje (APC – Tsafe ta Gabas) ya gabatar da kudirin a kan bukatar gwamnan na tantancewa tare da tabbatar da sunayen wadanda ya naɗa.

Kara karanta wannan

Ministan Buhari Ya Ya Ja Kunnen Gwamnatin Tinubu Kan Hambarar da Bazoum a Nijar

Shugaban marasa rinjaye na majalisar, Malam Aliyu Ango (APC – Talata-Mafara ta Kudu) ne ya goyi bayan kudurin, kamar yadda PM News ta rahoto.

Nijar: "Kada Ka Jefa Yankin Sahara Cikin Yaƙi" Sheikh Rijiyar Lemu Ga Tinubu

A wani labarin kuma Sheikh Muhammad Sani Rijiyar Lemu ya buƙaci shugaba Tinubu ya guje wa ɗaukar matakin soji kan gwamnatin sojin Nijar.

Malamin ya ce ya kamata Najeriya ta yi tunani a kan dangantakar da ke.tsakaninta da ƙasar da kuma al'ummar jamhuriyar Nijar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262