Fadar Shugaban Kasa ta fadi abin da zai hana a damka shugabanci a hannun Bola Tinubu

Fadar Shugaban Kasa ta fadi abin da zai hana a damka shugabanci a hannun Bola Tinubu

  • Fadar shugaban kasa ta fadawa Jam’iyyun PDP da LP cewa Bola Tinubu zai karbi mulkin kasa
  • Malam Garba Shehu ya ce babu abin da zai hana Tinubu ya shiga Aso Villa sai hukuncin kotu
  • Zababben Shugaban Najeriyan da bakinsa ya taba cewa ba za a soke zaben 2023 kamar a 1993 ba

Abuja - Fadar shugaban kasa ta jaddada cewa nasarar Bola Ahmed Tinubu a zaben shugaban kasa tana nan, sai dai idan kotu ta ce ba haka ba.

Vanguard ta rahoto Mai taimakawa shugaban Najeriya wajen yada labarai da hulda da jama’a, Malam Garba Shehu yana mai wannan maganar.

Garba Shehu ya bayyana haka a rubutun da ya yi domin nuna nasarorin da Muhammadu Buhari ya samu da ya ziyarci birnin Doha a Qatar.

Mai magana da yawun na shugaba Muhammadu Buhari ya ce masu sukar INEC a game da zaben bana, su na fadan abin da suka ga dama ne.

Kara karanta wannan

Ba mu yarda ba: Yarbawa sun ce Tinubu bai ci zabe ba, sun fadi wanda ya lashe zaben bana

Buhari ya yi banza da masu surutai

Hadimin ya ce shugaban kasa ba zai yi abin da zai iya taba martabar zaben da aka gudanar ba.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

An rahoto Garba Shehu yana cewa Mai gidansa ya yi kunnen uwar-shegu ga masu wadannan surutai a Najeriya ne ta hanyar fita zuwa kasar waje.

Tinubu
Tinubu da Buhari Hoto: @officialasiwajubat
Asali: Facebook

A rubutun da ya yi, Mai magana da yawun shugaban ya ce mai ja da sakamakon zaben, ya garzaya kotun korafin zabe domin ya shigar da kara.

Punch ta ce fadar shugaban kasa ta na zargin wadanda suke tir da zaben shugaban kasar da aka yi a Fubrairun 2023 su da wata muguwar manufa.

Maganar da Garba Shehu ya yi

"Nasarar Bola Tinubu a zabe ta na nan. Idan ka fusata, kuma dama ka na da hakki, sai ka tafi kotu.

Kara karanta wannan

Hukumar INEC ta mamayi Shugaban Kasa, an daga zaben Gwamnoni bai da labari

Burin hakan shi ne a jefa mutane a cikin razani, a jawo firgici a cikin al’umma, a bata sunan gwamnati.
Masu wannan tunani su na ganin za a iya dawo da rikicin Yunin 1993, mafi muni bayan yakin basasa.
Wadanda ke wannan sun manta da abin da zababben shugaban kasar ya fada a fadar Gbong-Gwon Jos.
Da ya je birnin domin bude kamfe, Tinubu ya ce ba za a soke zabe ba ko wanene zai zama shugaban kasa."

- Garba Shehu

Yadda Tinubu ya ci zabe - Sanata Iyiola Omisore

An samu labari Sakataren APC, Iyiola Omisore ya ce hadin-kan ‘Yan APC ya jawo Bola Tinubu ya iya dankara Atiku Abubakar da Peter Obi da kasa.

Sanata Iyiola Omisore ya karyata ‘Yan takaran PDP da LP, ya ce ba ayi magudin zabe ba ganin yadda APC ta rasa Katsina, Nasarawa, Filato da Legas.

Kara karanta wannan

Sai Da Na Dage Da Addu'a Don Kawai Allah Ya Ba Tinubu Nasara, Gwamnan APC Ya Magantu

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng