Matar Abiola Ta Kai Karar Shugaban ‘Yan Sanda, Tana Neman Naira Biliyan 100 a Kotu

Matar Abiola Ta Kai Karar Shugaban ‘Yan Sanda, Tana Neman Naira Biliyan 100 a Kotu

  • Farfesa Zainab-Duke Abiola ta na so kotu ta umarci jami’an ‘yan sanda su biya ta Naira Biliyan 100
  • Matar MKO Abiola tana neman diyyar N100bn saboda zargin bata mata suna da ‘yan sanda suka yi
  • Zainab-Duke Abiola ta ce an bata mata suna ta hanyar hada-kai da dogarinta, wajen shirya kazafi

Abuja - Farfesa Zainab-Duke Abiola, daya daga cikin matan Marigayi Cif MKO Abiola, ta shigar da karar shugaban ‘yan sandan Najeriya a wata kotun tarayya.

A rahoton da Vanguard ta fitar, an fahimci cewa Farfesa Zainab-Duke Abiola tana karar Sufetan ‘yan sandan da wasu mutane hudu a kotun tarayya a Abuja.

Mai karar tana tuhumar yaron Sufetan ‘yan sanda, Ibrahim Alkali da Teju Moses wanda ya yi aiki a matsayin babban 'dan sandan da ke aikin ba ta tsaro.

Kara karanta wannan

Asiri Ya Tonu: An Kama Wani Mai Hannu a Harin Jirgin Kasan Kaduna-Abuja, An Gano Abu 3

Zainab-Duke Abiola ta fadawa kotu wadannan mutane sun hada-kai da Teju Moses a lokacin shi ne dogarinta, sun yi mata sharrin cin zarafin Ibrahim Alkali.

Ba ayi mani adalci ba - Zainab-Duke Abiola

Farfesa Abiola tayi tir da ‘yan sanda na kin binciken lamarin da kyau, sai kurum suka gabatar da ita a gaban manema labarai a matsayin wanda tayi laifi.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

A watan Satumban 2022, jami’an tsaro suka gabatar da mai dakin Marigayin da sunan gwabje wani. Abiola ta ce zargin da ake yi mata, ba gaskiya ba ne.

Matar Abiola
Yemi Osinbajo da iyalin IGP Hoto: yemiosinbajo.ng
Asali: UGC

Kamar yadda rahoto ya zo daga gidan talabijin Channels, Tawo Tawo ne Lauyan da ya shigar da kara mai lamba FHA/ABJ/CS/2370/202 a madadin Farfesan.

Tawo Tawo (SAN) yake cewa zargin da ake jefi Duke Abiola ya bata mata suna da mutunci, a dalilin haka ta bukaci Alkali ya bada umarni a biya ta N100m.

Kara karanta wannan

An Samu Rashin Jituwa a Jam’iyyar LP, Jagorori Za Suyi Fito na Fito da Peter Obi

“Wannan lamari ya jawo mani matsala, tashin hankali da rashin lafiya, kuma ya bata sunana da mutuncina a Duniya, duk da irin matsayin da na kai a Duniya.
Shi Ibrahim Alkali ya hada-kai da tsohon dogari na, ya yi karyar na ci masa zarafi. Idan an je kotu, mu na da kyamarar CCTV da zai nuna abin da ya faru.”

- Farfesa Zainab-Duke Abiola

Nan da ranar 28 ga watan Fubrairun 2023, Alkali zai zartar da hukunci a kotun mai zama a Abuja.

Farashin man fetur

Ku na da labari Gwamnati ta ce babu maganar karin farashi a Najeriya duk da wahalar fetur ya karu sosai, musamman a 'yan kwanakin bayan nan.

Shugaba Muhammadu Buhari bai amince da karin kudin fetur a lokacin nan da ake cikin wahala ba., Ministan fetur yace Buhari ya damu da halin talaka.

Asali: Legit.ng

Online view pixel