Hotunan Atiku Da Okowa Yayin da Suka Ziyarci Mahaifiyar Marigayi Yar’adua, Hajiya Aya Dada a Katsina

Hotunan Atiku Da Okowa Yayin da Suka Ziyarci Mahaifiyar Marigayi Yar’adua, Hajiya Aya Dada a Katsina

  • Alhaji Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa na PDP da abokin tafiyarsa, Ifeanyi Okowa sun kai ziyarar ban girma ga Hajiya Aya Dada
  • Yan takarar na PDP sun ware lokaci sun je ganin mahaifiyar marigayi shugaban kasa Umaru Musa Yar'adua yayin da suka je kamfen a jihar Katsina
  • Yan Najeriya da dama sun yi farin ciki da ganin dattijuwar matar yayin da suka yi mata addu'an tsawon rai cikin koshin lafiya

Katsina - Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar da abokin takararsa, Ifeanyi Okowa sun ziyarci mahaifiyar marigayi tsohon shugaban kasa, Umaru Musa Yar’adua a Katsina.

Yan takarar sun ziyarci Hajiya Aya Dada ne a ranar Talata, 20 ga watan Disamba yayin da suka je jihar don yakin neman zabensu.

Atiku, Okowa da mahaifiyar Yar'adua
Hotunan Atiku Da Okowa Yayin da Suka Ziyarci Mahaifiyar Marigayi Yar’adua, Hajiya Aya Dada a Katsina Hoto: Governor Ifeanyi A. Okowa
Asali: Facebook

Da yake wallafa hotunan ziyarar tasu a shafinsa na soshiyal midiya, Okowa ya bayyana dattijuwar matar a matsayin mai zuciyar alkhairi inda ya roki Allah da ya albarkaceta tare da kara mata tsawon rai.

Kara karanta wannan

Shirin 2023: Tashin hankali ga Tinibu, Atiku ya samu wata ganawa da Kiristocin wata jihar Arewa

Ya rubuta:

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

"Hajiya Aya Dada, mahaifiyar tsohon shugaban kasa, marigayi Umaru Yar’adua da Tafida Shehu Musa Yar’Adua ta kasance uwa ga mutane da dama. Babban zuciyanta ya tarbi shugabanni da dama daga jam’iyyun siyasa daban-daban.
“Wannan ne dalilin da yasa a safiyar yau, nake alfaharin jerawa da dan takarar shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar wajen kaiwa Hajiya Aya Dada ziyara a mahaifarta da ke Katsina.
“Muna rokon Allah ya ci gaba da yi mata albarka da kuma barinta a raye. Ameen!”

Ga wallafar tasa a kasa:

Jama’a sun yi martani

Chiedu Ikechukwu ya yi martani:

"Hakan ya yi kyau kuma ya dace, Jihar Katsina sun gaji da wahala da matsin rayuwa na APC sannan suna bukatar AtikuOkowa don ceto su, PDP ta shirya ceto Najeriya mulkin zalunci na APC, Katsina ta shirya, Najeriya ta shirya, AtikuOkowa sun shirya tsaf."

Kara karanta wannan

Jam'iyyar APC Ta Samu Gagarumin Tagomashi, Dubban Mutane Sun Sauya Sheka A Jihar Sokoto

Emmanuel Junior Zakka ya ce:

"Zuciyata ta yi nauyi a nan. Allah ya ja da ran kaka cikin koshin lafiya. Allah ya albarkaci mai hada kan kasa kan wannan ziyarar.
"Ba za ta mutu ba har sai ta shaida rantsar da ku, da izinin Allah."

Rukevwe Inije ta ce

"Wow, godiya ga AtikuOkowa da kuka nuna kauna ga ahlin Yar'adua, na san mahaifiyar tsohon shugaban kasar Najeriya za ta yi farin ciki sosai da ganin tawagar ceto. AtikuOkowa sun damu saboda a matsayin daya za mu cimma abubuwa. Ku zabi AO2023."

Omoh Eduvie ta ce:

"Danta, tsohon shugaban kasar Najeriya ya kasance mutumin kirki wanda ke nufin yan Najeriya da alkhairi kafin mutuwa ta dauke shi, ta tarbiyantar da shi sosai, mama Allah ya ja da ranki cikin koshin lafiya."

Shema ba zai yiwa Atiku Kamfen ba

A gefe guda, mun ji a baya cewa tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema basa tare da yakin neman zaben Atiku Abubakar saboda banbancin da ke tsakaninsu da dan takarar gwamnan PDP a jihar, Sanata Yakubu Lado Danmarke.

Kara karanta wannan

Kwabar Atiku ta yi ruwa, ya rasa manyan shugabannin PDP a wata jihar Arewa

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Online view pixel