Murnar Tinubu Za ta Koma Ciki, Daliban Najeriya Sun Karyata Batun Goyon Bayansa
- Shugabannin NANS na jihohin Yarbawa sun ce ba suyi wa wani ‘Dan takaran 2023 mubaya’a tukuna ba
- Kungiyar daliban tace sai ta duba manufofin masu neman zama shugaban kasa, sai ta dauki matsaya
- A baya an ji labarin wasu dalibai na cewa Bola Tinubu da Kashim Shettima na APC za su ba kuri’arsu
Lagos - Kungiyar daliban Najeriya watau NANS na shiyyar Kudu maso yamma ta nesanta kan ta daga maganar yi wa wani ‘dan takaran 2023 mubaya’a.
Tribune ta fitar da rahoto a ranar Alhamis, aka ji shugaban shiyyar da wasu mataimakansa su na cewa ba su goyon bayan kowa a zaben Najeriya.
Shugaban kungiyar, Emmanuel Adegboye da mataimakinsa, John Alao da Kakakin kungiyar, Opeoluwa Awoyinfa sun saki jawabi ga manema labarai.
Babu ruwanmu da Tinubu/Shettima Students Vanguard

Kara karanta wannan
Shugaban Yarbawa ya tona asirin Tinubu, ya fadi wata babbar illarsa da yasa ba zai zabe shi ba
A jawabin da aka fitar, kungiyar daliban Najeriyar tace ba ta san da zaman wata Tinubu/Shettima Students Vanguard ko makamancinta a tafiyarta ba.
‘Yan Tinubu/Shettima Students Vanguard ne aka ji suna ikirarin dalliban kasar nan suna tare da tikitin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da Kashim Shettima.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Shugabannin NANS na Kudu maso yamma sun ce ba su kauce hanyar magabatansu, da za su goyi bayan zalunci da shugabannin da ke mulki suke yi ba.

Source: Twitter
Kafin mu fito da 'dan takaranmu... - NANS
Kungiyar tace ba ta raba kan ta da siyasa, tana sha’awar ganin wa zai karbi mulki a 2023, amma zuwa yanzu ba ta fitar da wanda za a zaba ba tukuna.
A rahoton Vanguard, kungiyar tace tana duba ‘yan takaran shugaban kasa ne domin ganin wanene manfufofinsa za su fi taimakawa dalibai idan ya ci zabe.
Wajen tsaida ‘dan takaran da za a zaba, NANS tace ba za ta nuna kwadayin dukiyar ‘yan siyasa ba, tare da kira ga masu neman mulki su daina kawo rudu.

Kara karanta wannan
2023: Ɗaliban Najeriya Sun Goyi Bayan Takarar Tinubu Da Shettima, Sun Bada Ƙwakwarar Dalili
Wannan karo daliban sun ce ya zama dole su nesanta kansu daga Tinubu/Shettima Students Vanguard, suka ce sam babu abin da ya hada ta da ‘ya ‘yanta.
Kwamred Adegboye da sauran shugabannin NANS suka ce wannan kungiya, hanyar wasu ne a gefe na tatsar kudi daga hannun ‘yan siyasa da sunan dalibai.
Sanatan PDP ya yabi Tinubu
Kun samu rahoto Chimaroke Nnamani wanda ya yi gwamna a Enugu a jam’iyyar PDP tun 1999, babu abin da yake fada a game da Bola Tinubu sai alheri.
An ji Sanata Nnamani yana cewa a lokacin da Tinubu yake gwamna, ya yi zarrra a kan duk sauran abokan aikinsa, saboda ya dauko masu kwakalwa.
Asali: Legit.ng