Kano 2023: INEC ta yi watsi da dan Abacha, ta zabi Wali ya yi takarar gwamna a PDP

Kano 2023: INEC ta yi watsi da dan Abacha, ta zabi Wali ya yi takarar gwamna a PDP

  • Jam'iyyar PDP a jihar Kano ta samu dan takarar gwamna, INEC ta fitar sunayen masu takarar gwamna a jihohin Najeriya
  • An samu hargitsi a PDP ta jihar Kano yayin da aka gudanar zaben fidda gwanin dan takarar gwamna a 203
  • An samu jihohin da aka samu rikicin cikin gida a jam'iyyu daban-daban na siyasa, lamarin da ke kawo rarrabuwar kai

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Kano - Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta ayyana suna tare da tantance Sadik Wali a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Kano.

Hakan ya haifar da rudani a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar da ke tsagin zartaswar jihar karkashin jagorancin Shehu Sagagi.

Daily Trust ta ruwaito cewa rikicin da ya barke a jam’iyyar ta Kano ya kai ga gudanar da zaben fidda gwani na jam’iyyar a tsagi biyu.

Kara karanta wannan

Buhari ga 'yan Najeriya: Ku zabi Tinubu don ci gaba da shan jar miyar da nake baku

INEC ta zabi wani, ta yi waje da dan Abacha
Kano 2023: INEC ta yi watsi da dan Abacha, ta zabi Wali ya yi takarar gwamna a PDP | Hoto: dailytrust.com
Asali: UGC

Hakan dai ya haifar da samun ‘yan takarar shugaban kasa mabambanta a jam'iyyar ta PDP mai adawa.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Kwamishinan zabe na jihar, Farfesa Riskuwa Shehu, ya shaida wa manema labarai a ranar 30 ga watan Yuni cewa hukumar ta sanya ido kan zaben fidda gwanin da Shehu Wada Sagagi ke jagoranta wanda ya samar da Abacha a matsayin dan takarar gwamna.

Amma sunayen da aka lika na 'yan takarar gwamna a ranar Juma’a a ofisoshin INEC na jihar, an gano, cewa an bayyana sunan Wali da na mataimakinsa Yusuf Dambatta a bangon ofishin INEC na Kano.

Da yake mayar da martani kan lamarin, jami’in hulda da jama’a na INEC na jihar Kano, Ahmad Adam Maulud, ya ce hukumar a matakin jiha ta mika abin da sakamakon zaben fidda gwanin ya samar ga hedikwatar ta kasa.

Kara karanta wannan

Ortom Bai Fadi Gaskiya Ba, Kwamitin PDP Bata kada Kuri’a Akan Daukan Abokin Takara na ba - Atiku

Ya ce abin da aka manna a bangon INEC ranar Juma’a shi ne abin da aka ya dawo daga hedikwatar INEC ta kasar.

A cewar jami'in:

"Mun tura abin da muka yi zuwa hedkwatarmu ta kasa kuma abin da muka manna a yau (Juma'a) ya fito ne daga gare su kai tsaye."
"Duk wanda ke son neman karin haske ya tuntubi cibiyar jam'iyyarsa ta kasa don samun bayanai."

Ta tabbata: INEC ta amince da takarar gwamnan Kano ga dan janar Abacha a PDP

A baya kunji cewa, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta tabbatar da cewa ta sa idon basira a zaben fidda gwani da ya samar da Mohammad Abacha a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Kano.

Kafin bayanin na INEC dai an yi ta cece-kuce kan wanda hukumar za ta amince da shi a matsayin dan takarar gwamna tsakanin Mohammed Abacha da Sadiq Wali.

Kara karanta wannan

2023: Sabon sabani ya kunno kai a APC kan wanda Tinubu ya zaba mataimaki, Gwamna El-Rufa'i ya fusata

Kwamishinan zabe na yanki (REC), Farfesa Riskuwa Shehu, ya tabbatar wa manema labarai hakan a Kano, a ranar Alhamis, 30 ga watan Yuni, in ji jaridar The Guardian.

Asali: Legit.ng

Online view pixel