Yadda ta kaya da Tinubu ya bayyana gaban kwamitin tantance masu neman takara a APC

Yadda ta kaya da Tinubu ya bayyana gaban kwamitin tantance masu neman takara a APC

  • A jiya kwamitin tantance masu takarar shugaban kasa ya zauna da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
  • Ahmed Tinubu ya yi bayanin abin da ya sa yake neman takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC
  • Bayo Adenuga ya ce mai takarar ya nuna irin zurfin ilminsa wajen sanin tattalin arzikin Najeriya

Abuja - A ranar Litinin, 30 ga watan Mayu, 2022, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya zauna gaban kwamitin da ke tantance ‘dan takarar shugaban kasa a PDP.

The Cable ta fahimci Asiwaju Bola Ahmed Tinubu yana cikin wadanda kwamitin da John Oyegun yake jagoranta ya fara tantancewa cikin masu neman takara.

Mutane 11 aka tantance a jiya, Bola Tinubu da mutanensa sun isa otel din a lokacin ana ruwan sama.

Shugaban kwamitin yakin neman zaben Tinubu, Bayo Adenuga ya bayyana cewa mai gidansa ya yi wa kwamitin APC bayanin abin da ya sa yake neman mulki.

Kara karanta wannan

Rochas Okorocha, Lawan da sauran yan takarar shugaban ƙasa 9 da Kwamitin APC zai tantance yau

A cewar Bayo Adenuga, Bola Tinubu ya kawo nasarorin da ya samu a lokacin da ya mulki jihar Legas a cikin dalilan da suka sa yake so jam’iyyar ta tsaida shi.

A jawabin da Adenuga ya fitar, ya bayyana cewa Tinubu ya burge ‘yan kwamitin a game da yadda ya rika amsa tambayoyin da aka yi masa, yana bayani da kyau.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Tinubu na neman takara a APC
Wajen tantance Bola Tinubu Hoto: www.thecable.ng
Asali: UGC

Jawabin Bayo Adenuga

“Wasu tambayoyin sun shafi tasowarsa, ilminsa da aikin da ya yi. Ya fadawa kwamitin cewa ya cancanci ya zama ‘dan takarar shugaban kasa a APC.”
“Ya bada misali da nasarorinsa a matsayin gwamnan jihar Legas, inda ya kara harajin da ake samu daga N600m a duk wata, yanzu ya zama N51bn a yau.”
“Ya kuma kawo yadda ya gayyaci Enron da suka zama kamfanin farko da suka fara samar da wuta a Najeriya, da yadda Najeriya za ta samu lantarki.”

Kara karanta wannan

Sanatan APC: Gwamna Wike ya yi kokari, shi ya ci zaben fidda gwani ba Àtiku ba a ra'ayina

“A amsoshin da ya bada, Tinubu ya nuna zurfin ilminsa a bangaren tsimi da fahimtar tattalin arziki.”
“Kwamitin tantancewar sun gamsu da ilmin Tinubu game da tattalin arzikin Najeriya da sha’anin zamantakewar rayuwar da ke addabar Najeriya.”

- Bayo Adenuga

Bayan an kammala tantance tsohon gwamnan na jihar Legas, jaridar ta samu labari cewa ya dauki hoto tare da John Oyegun da sauran ‘yan kwamitin APC.

Takarar Atiku a PDP

Dazu kun ji cewa Gwamnoni jihohi biyu ake kawowa a lissafin wanda za su iya takarar mataimakin shugaban kasa PDP, su na shirin barin mulki.

Daga ciki akwai Gwamna Udom Emmanuel wanda ya nemi tikitin shugaban kasa a PDP, amma duk da haka Wazirin Adamawa na tunanin tafiya da shi.

Asali: Legit.ng

Online view pixel