Wannan irin hadi haka! Martanin yan Najeriya bayan dan El-Rufai ya fitar da hoton mahaifinsa da Tinubu
- Jama'a sun tofa albarkacin bakunansu bayan bayyanar hoton jagoran APC, Bola Tinubu da gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai
- Wasu na ganin El-Rufai ma ya bi, inda wasu ke ganin shi za a tsayar a matsayin abokin takarar tsohon gwamnan na Lagas a 2023
- Dan El-Rufai, Bello shine ya fitar da hoton wanda ya ja hankalin jama'a sosai
Yayin da ake tsaka da cece-kucen siyasa a jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki, wani hoton Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna zaune tare da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya bayyana a shafin Twitter.
Dan gwamnan na jihar Kadunam Bello-El-Rufai ne ya wallafa hoton wanda ya samu martani daban-daban daga yan Najeriya a ranar Alhamis, 24 ga watan Maris.
Tinubu, tsohon gwamnan jihar Lagas, ya ayyana aniyarsa ta son yin takarar kujerar shugaban kasa a babban zaben 2023.
Yayin da akalla gwamnoni uku suka fito suka ayyana goyon bayansu ga jigon na APC, Gwamna El-Rufai da wasu gwamnoni da dama a karkashin jam’iyyar basu fito sun nuna goyon bayan kowani dan takara.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Saboda haka, wallafa hoton jagororin na APC biyu da Bello ya yi, ya haifar da rade-radi. Yayin da wasu ke kallon hoton a matsayin El-rufai na goyon bayan kudirin Tinubu, wasu na hasashen ko gwamnan na Kaduna na iya zama abokin takarar tsohon gwamnan na Lagas.
Shuraim Abubakar , @shuraim, ya rubuta:
“Da fatan ba wannan bane hadin a 2023.”
A martaninsa, Olajide Balogun,@olajt, ya rubuta:
"Shhh!!! Ku bari su ta cinka-cinka.”
A. A. Alhaji, @AZ_BinBaz, yace:
“Irin wannan hadi haka!!!"
#ThankASoldier, @DipoSpeak, ya ce:
“Wannan hadin zai yi ma’ana, wasu ba za su iya bacci ba daga yanzu, za su aiwatar da manufa da dama kuma zai yi fice. Muna lura sosai."
Dr. Ahmad, @Ahmad_ismaillll, ya ce:
"Wannan hadin zai yi kyau ga Najeriya BAT2023✔️"
TAH-LI-KAH, @freetalkerr, ya ce:
"Basa fada ne kuma????"
Bonaparte, @abba_mashasha, ya ce:
"A yanzu da aka kara elrufaiina cikin wannan tafiya ina fatan zai zaba mataimakin shugaban kasa 2027"
Hadimin El-Rufai Ya Koma Jam'iyyar PDP, Zai Yi Takarar Gwamna a 2023
A wani labari na daban, mun ji cewa Jimi Lawal, Mashawarci na muamman ga gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan habbaka saka hannun jari, ya shiga jam'iyyar PDP a Jihar Ogun., rahoton Daily Trust.
Lawal, wanda ya ziyarci sakatariyar PDP a Abeokuta, ranar Asabar, ya kuma ayyana niyarsa na yin takarar gwamna a zabe da ke tafe.
Ma'aikacin bankin da ya samu horaswa a Landan ya nemi kujerar gwamna a karkashin APC a zaben 2019, amma ya sha kaye hannun Gwamna Dapo Abiodun.
Asali: Legit.ng