Abun bakin ciki: Jam’iyyar PDP ta sake rashi na wani babban jigonta

Abun bakin ciki: Jam’iyyar PDP ta sake rashi na wani babban jigonta

  • Babban jigon jam'iyyar PDP a karamar hukumar Ughelli ta arewa da ke jihar Delta, Cif Lawrence Agbatutu, ya mutu
  • Kakakin Gwamna Ifeanyi Okowa ne ya sanar da labarin mutuwarsa a ranar Litinin, 22 ga watan Nuwamba
  • Zuwa yanzu jam'iyyar adawar kasar bata fitar da wani bayani ba game da mutuwar jigon nata a hukumance

Jihar Delta - Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta sake rashi na wani jigonta a jihar Delta, Cif Lawrence Agbatutu.

Har zuwa mutuwarsa, marigayin ya kasance shugaban PDP a karamar hukumar Ughelli ta arewa da ke jihar.

Abun bakin ciki: Jam’iyyar PDP ta sake rashi na wani babban jigonta
Abun bakin ciki: Jam’iyyar PDP ta sake rashi na wani babban jigonta Hoto: Ovie Success Ossai
Asali: Facebook

Ovie Success Ossai, daya daga cikin hadiman Gwamna Ifeanyi Okowa, ya sanar da hakan a shafinsa na Facebook a safiyar ranar Litinin, 22 ga watan Nuwamba.

Ya ce:

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kara karanta wannan

Gaba da gaban ta: Bidiyo da hotunan Tinubu ya na jinjina, gurfane gaban Aminu Dantata

“Yanzun nan muka rasa shugaban PDP a karamar hukumar Ughelli ta arewa, Hon. Lawrence Agbatutu. Allah ya ji kansa.”

Yan kwanakin baya, wani dan takarar gwamna kuma tsohon kwamishinan tattalin arziki a karkashin gwamnatin Dr Emmanuel Uduaghan, Cif Kenneth Okpara, ya mutu.

Kafin nan, mambobin majalisar jihar Delta biyu daga Isoko ta arewa da kudu sun mutu a farkon shekarar nan.

Hadimar Okowa, Mary Iyasere itama ta mutu yan makonnin da suka gabata a Delta.

A halin da ake ciki, ana sauraron jin rahoton mutuwar a hukumance daga iyalan marigayin.

Ni da mahaifiyata muna kallo lokacin da aka zare ran kanina amma babu yadda muka iya - Dangote

A wani labarin, mun kawo a baya cewa mai kudin Afrika, Alhaji Aliko Dangote, ya magantu a kan rasuwar kaninsa, Alhaji Sani Dangote.

Marigayin wanda ya kasance mataimakin shugaban rukunin kamfanonin Dangote, ya rasu a ranar Lahadi, 14 ga watan Nuwamba, a kasar Amurka bayan ya yi jinya.

Kara karanta wannan

Hankula sun tashi a jihar Nasarawa kan kisan wasu makiyaya

Da ya tarbi jagoran jam'iyyar All Progressives Congress (APC), Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a gidansa da ke Kano, a ranar Juma'a, 19 ga watan Nuwamba, Dangote ya ce mahaifiyarsu da yaran Sani na a wajen da aka dauki ran marigayin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng