Iran/Isra’ila: Bama Bamai Sun Hana ’Yan Najeriya Sakat, Ana Kokarin Tsamo Su

Iran/Isra’ila: Bama Bamai Sun Hana ’Yan Najeriya Sakat, Ana Kokarin Tsamo Su

  • Gwamnatin Najeriya ta bayyana kokari da ta ke yi wurin ganin ta kwashe 'yan kasar da suka makale a Gabas ta Tsakiya
  • Ta ce tana kokarin dawo da ‘yan Najeriya da suka gaza samun damar fitowa a Iran da Qatar sakamakon rikicin yankin
  • Ma’aikatar harkokin waje ta ce ana fuskantar kalubalen sufuri da sharuddan shiga Armenia wajen fitar da ‘yan Najeriya daga Iran

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bayyana cewa tana kokarin tabbatar da tsaron ‘yan Najeriya da suka makale a Gabas ta Tsakiya.

'Yan Najeriya da dama na makale a kasashen Qatar da Iran sakamakon rikicin da ya barke a yankin Gabas ta Tsakiya.

Najeriya ta nuna damuwa kan yan kasar da ke makale a Gabas ta Tsakiya
Jagoran addini a Iran, Ali Khamenei, Bola Tinubu da Benjamin Netanyahu. Hoto: @khamenei_ir, Bayo Onanuga, Benjamin Netanyahu.
Source: Facebook

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin waje, Kimiebi Ebienfa shi ya tabbatar da haka ga wakilin Punch a Abuja.

Kara karanta wannan

Ta leko ta koma: Kasashe sun ki karbar jakadun Najeriya da Tinubu ya tura

Abin da gwamnati ke yi wa yan Najeriya

Ebienfa ya ce gwamnatin na bai wa ‘yan Najeriya da ke wuraren da rikici ya fi tsanani fifiko, musamman wadanda ke Iran da kuma Israel.

Ma’aikatar ta ce tana nazarin hanyoyi daban-daban domin taimaka wa ‘yan kasar da abin ya shafa, tare da rokon su da su yi hakuri yayin da ake shirin dawo da su gida.

A cewarsa, wadannan wurare ne da ake fama da hare-haren makamai masu linzami da bamabamai, wanda ya kara wahalar da shirin kwashe mutane zuwa wurare masu tsaro.

Ebienfa ya bayyana cewa fitar da ‘yan Najeriya daga Iran na fuskantar kalubalen sufuri, musamman wajen jigilar su zuwa iyakar Armenia.

Ya ce wasu kamfanonin sufuri a Iran na taka-tsantsan wajen samar da motocin bas da za su dauki daliban Najeriya daga jami’o’i zuwa iyakar Armenia.

Haka kuma ya ce hukumomin Armenia sun gindaya sharadi cewa duk wanda zai shiga kasarsu dole ne ya nuna hujjar tikitin fita daga kasar.

Kara karanta wannan

Najeriya ta kai wa mutanenta da suka makale a yaƙin ƙasar Iran agaji

Ebienfa ya kara da cewa gwamnati na duba hanyoyin tallafa wa daliban da suka makale, ciki har da samar musu da abinci, kudaden gaggawa da kuma tufafin sanyi saboda yanayin sanyi.

Gwamnatin Tinubu ta damu kan halin da yan Najeriya ke ciki a Gabas ta Tsakiya
Shugaba Bola Tinubu na Najeriya yayin taro a fadar shugaban kasa. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Twitter

Matsalar da 'yan Najeriya suka samu

Game da ‘yan Najeriya da suka makale a Doha a Qatar, Ebienfa ya ce yawancinsu fasinjojin wucewa ne da jiragensu suka samu tangarda.

Ya ce kamfanin jirgin sama na 'Qatar Airways' ya samar masu da masauki a otal otal tare da abinci sau uku a rana.

A cewarsa, jami’an ofishin jakadancin Najeriya a Doha sun ziyarci ‘yan Najeriya da suka makale domin karfafa musu gwiwa da kuma duba hanyoyin da za a dawo da su gida.

Ya kara da cewa daya daga cikin hanyoyin da ake tunani ita ce dawowar wasu jiragen Qatar kadan-kadan, wanda idan aka saka Najeriya a cikin wuraren da za su je, hakan zai taimaka wajen dawo da ‘yan Najeriya gida.

Najeriya ta tsoma baki a rikicin Iran/Isra'ila

An ji cewa Gwamnatin tarayya ta fitar da gargadin tsaro ga ’yan Najeriya mazauna Iran da kasashen Gulf ana tsaka da rigima.

Kara karanta wannan

Sheikh Gumi ya tona asirin gwamnati, ya fadi abin da suka sani kan ta'addanci

Wannan sanarwa ya biyo bayan kai hare-haren Amurka da Isra’ila kan Iran da ya tayar da hankali a yankin Gabas ta Tsakiya.

Ma’aikatar Harkokin Waje ta ce tana sa ido kan rikicin da ke kara kamari, tare da shawartar jama’a su guji wuraren sojoji da taruka.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.