ICPC: Lauyan El Rufa'i Ya Yi Martani kan 'Gano' Gidajen Tsohon Gwamna a Kasar Masar

ICPC: Lauyan El Rufa'i Ya Yi Martani kan 'Gano' Gidajen Tsohon Gwamna a Kasar Masar

  • Lauyan tsohon gwamnan Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufai, ya zargi ICPC da yin abin da ya kira tsangwamar siyasa
  • Ya ce rahotannin da ke cewa El-Rufai na da kadarorin biliyoyin Naira a Masar magana ce kawai da zummar ci gaba da rike shi
  • Lauyan ya ce tsare 'dan siyasar sama da kwanaki 20 ba tare da tuhuma ba ya saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kaduna – Lauyan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufai, Ubong Esop Akpan, ya zargi ICPC da gudanar da abin da ya kira tsangwamar siyasa a kan tsoron gwamna.

Ubong Esop Akpan ya yi wannan bayani ne bayan wasu rahotanni sun bayyana cewa El-Rufai na da kadarori na biliyoyin Naira a kasar Masar.

Kara karanta wannan

ICPC ta gano wasu gidajen alfarma da ake zargin El Rufai ya mallaka a ƙasar waje

Lauyan El-Rufa'i ya karyata rahoto a kan tsohon gwamna
Tsohon gwamnan Kaduna Nasir El-Rufa'i Hoto: Nasir El-Rufai
Source: Facebook

Daily Trust ta wallafa cewa wadanda aka ce an gano su ne yayin binciken da hukumar ke yi kan shekarun da ya yi yana gwamna.

Lauyan Nasir El-Eufa'i ya dura kan ICPC

Daily Post a wallafa cewa wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, 9 ga watan 2026 Akpan ya bayyana zarge-zargen da cewa ba su da tushe ko makama.

Ya kara da cewa rahotannin da ake yadawa a kafafen yada labarai sun dogara ne da majiyoyin da ba a bayyana sunayensu ba, kuma ba su da wata hujja mai tabbaci da za a iya tantancewa.

Lauyan El-Rufai ya zargi ICPC da bita da kulli
Jigo a jam'iyyar adawa ta ADC, Nasir El-Rufa'i Hoto: ADC Party
Source: Twitter

Lauyan ya kuma ce zarge-zargen wani bangare ne na abin da ya kira shirye-shiryen bata suna da aka tsara domin bata sunan El-Rufai a idon jama’a.

A cewarsa, manufar irin wadannan rahotanni na jawo goyon bayan jama’a domin ci gaba da tsare tsohon gwamnan.

Lauyan El-Rufa'i ya dura kan EFCC

Kara karanta wannan

Dalilin gidan gyaran hali na cigaba da tsare Abba Kyari duk da hukuncin kotu

Akpan ya bayyana cewa tun daga daren ranar 18 ga Fabrairu, 2026 ne ake tsare da El-Rufai, bayan wasu jami’an tsaro dun damka shi a hannun hukumar EFCC.

Ya ce kafin hakan, tsohon gwamnan ya mika kansa ga EFCC da kansa a ranar 16 ga Fabrairu domin amsa tambayoyi, kuma daga baya aka ba shi beli na wucin gadi kafin a mayar da shi ga ICPC.

Lauyan ya ce ci gaba da tsare shi sama da kwanaki 20 ba tare da gurfanar da shi a gaban kotu ba ya saba wa sashe na 35 na kundin tsarin mulkin Najeriya na shekarar 1999.

Akpan ya kuma bayyana shakku a kan sahihancin umarnin tsarewa na kwanaki 14 da aka ce wata kotun majistare ta bayar a ranar 19 ga Fabrairu.

Ya kara da cewa umarnin ya kare ne a ranar 4 ga Maris, kuma ba a taba mikawa El-Rufai ko lauyoyinsa ba.

An gano kadarori masu alaka da El-Rufa'i

A baya mun wallafa cewa hukumar ICPC ta gano wasu manyan kadarori a ƙasar Masar da ake zargin suna da alaƙa da tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai.

Kara karanta wannan

Akwai yiwuwar tsohon ministan Tinubu ya yake shi, yana kus kus da kusoshin adawa

Rahotanni sun nuna cewa an sayi kadarorin ne tsakanin shekarun 2021 zuwa 2023 a wasu unguwanni masu tsada da gine-ginen alfarma na New Cairo.

Ana binciken gidajen alfarmar da gidajen haya da dama a wurare irin su Arabella Estate, Banafsek Estate, Oriana Estate da Cairo Festival City da aka danganta da El-Rufa'i.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng