Kano: An Takaita Zirga Zirga, Mabiya Kwankwaso da Abba za Su Fafata a Zabe

Kano: An Takaita Zirga Zirga, Mabiya Kwankwaso da Abba za Su Fafata a Zabe

  • Rundunar 'yan sanda ta sanar da takaita zirga-zirga a kananan hukumomin Birni da Ungogo yayin da ake shirin zaben cike gibi a jihar Kano
  • Hukumar zabe ta kasa (INEC) ta sanar da cewa a gobe Asabar, 1 ga Fabrairu za a gudanar da zaben cike gibi a Kano, Abuja da sauransu
  • Wannan ne karon farko da bangaren Sanata Rabiu Kwankwaso da Abba Kabir Yusuf za su fafata a zabe bayan sauya shekar gwamnan

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Kano - Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta sanar da takaita zirga-zirga a kananan hukumomin Birni da Ungogo gabanin zaɓen cike gibi na majalisar jiha da za a gudanar a ranar 21 ga Fabrairu, 2026.

Sanarwar ta biyo bayan taron kwamitin shawarwari na hukumomin tsaro a lokacin zabe (ICCES), wanda kwamishinan INEC a Kano, Zango Abdu, ya jagoranta.

Kara karanta wannan

'Yan sanda sun cafke tsohon hadimin Buhari yayin da El Rufa'i ke tsare

CP Ibrahim Adamu Bakori
Kwamishinan 'yan sandan Kano na hira da 'yan jarida. Hoto: Abdullahi Haruna Kiyawa
Source: Facebook

Legit Hausa ta gano cewa kakakin rundunar 'yan sandan jihar ya wallafa a Facebook cewa a ranar 19 ga Fabrairu, 2026 kwamitin ICCES ya yi zama a Kano.

An shirya gudanar da zabe a Kano

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan jihar, CSP Abdullahi Kiyawa, ya fitar rundunar ta sanar da cewa ta takaita zirga-zirga a jihar.

Kiyawa ya bayyana cewa:

“ICCES ta kammala shirye-shiryen tsaro gabanin zaɓen cike gibi da za a yi a mazabun Birni da Ungogo a ranar 21 ga Fabrairu, 2026.”

Mataimakin shugaban ICCES kuma kwamishinan ’yan sanda, Ibrahim Adamu Bakori, ya sanar da mazauna yankunan cewa:

“Tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro, an ɗauki dukkan matakan da suka dace domin tabbatar da zaman lafiya da gudanar da zaɓe cikin ’yanci, adalci a mazabun Birni da Ungogo.”

Kara karanta wannan

Mummunar gobara ta sake sake tashi rigi rigi a wata babbar kasuwa a Kano

An takaita zirga zirga a Kano

Sanarwar ta ce an haramta zirga-zirgar motoci, adaidaita sahu da babura daga ƙarfe 12:00 na dare zuwa ƙarfe 6:00 na yamma a ranar Asabar, 21 ga Fabrairu, 2026, wadda ita ce ranar zaɓe.

Punch ta wallafa cewa sanarwar ta ƙara da cewa:

“Sai dai za a ba da izini ga motocin da ke aikin gaggawa kamar motar asibiti, motar kashe gobara da motocin jami’an zaɓe da masu sa ido da aka tantance.”

A cewar rundunar, masu kaɗa ƙuri’a da suka cancanta kaɗai za a bari a wuraren zabe, yayin da wakilan jam’iyyun da INEC ta tantance kaɗai za su samu izinin kasancewa a wuraren zaɓe.

Haka kuma, ta ce ba za a ba kungiyoyin tsaro na jiha kamar ’yan banga, Neighbourhood Watch, Hisbah, jami’an KAROTA da sauransu damar kasancewa a wuraren zaɓe ba.

Abba da Kwankwaso za su fafata

Wannan shi ne karon farko da za a gwada karfin siyasa tsakanin gwamna Abba Kabir Yusuf da ya koma APC da kuma Sanata Rabiu Kwankwaso da ya ke NNPP.

Kara karanta wannan

Gwamna ya fusata da rigimar APC ta lakume rayukan mutane 2, ya ba da umarni

Abba Kabir Yusuf da Rabiu Kwankwaso
Gwamna Abba Kabir Yusuf tare da Rabiu Musa Kwankwaso a Kano. Hoto: Saifullahi Hassan
Source: Facebook

Abba Kabir Yusuf ya shafe shekaru tare da Rabiu Kwankwaso kafin daga bisani su raba hanya a siyasance bayan samun mukamin gwamna.

Jihohin da za a yi zabe a 2026

A wani labarin, mun kawo muku cewa hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) ta sanar da cewa za ta gudanar da zabe a wasu jihohi da yankuna.

A ranar Asabar, 21 ga watan Fabrairun 2026 INEC za ta gudanar da zaben cike gibi a jihohin Kano da Rivers da na kananan hukumomi a Abuja.

Rahotanni sun bayyana cewa idan shekarar 2026 ta kara nisa, hukumar zabe za ta gudanar da zaben gwamna a jihohin Osun da Ekiti.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng