Ramadan 2026: Fitar Maniyyi da Wasu Abubuwa 6 da Ke Lalata Azumi

Ramadan 2026: Fitar Maniyyi da Wasu Abubuwa 6 da Ke Lalata Azumi

Yayin da aka fara azumin Ramadan na shekarar 2026, al'ummar Musulmi sun dukufa wajen neman lada da dukkan falalar da ke cikin wannan wata mai albarka.

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Azumi na ɗaya daga cikin manyan ibadu, wanda ya ƙunshi kame kai daga sha'awoyi kamar na abinci, abin sha, saduwa da iyali da tsakar rana da sauran abubuwan da ke ɓata shi.

Akwai jerin abubuwa 7 da ke lalata azumin watan Ramadan.
Wani mutumi da mata 2 suna karatun Al-Kur'ani. Hoto: LV4260 via Getty Images
Source: Getty Images

Abubuwa 7 da ke karya azumi a Ramadan

Ga jerin abubuwa bakwai da ke ɓata azumi a Ramadan, kamar yadda jami'ar UMS ta rahoto a shafinta na intanet:

1. Cin abinci ko shan ruwa da gangan

Yin hakan da gangan a cikin ranar Ramadan yana ɓata azumin Musulmi. Allah ya bayyana a Suratul Baqarah cewa a ci, a sha har alfijir ya keto, sannan a cika azumi har zuwa dare.

Kara karanta wannan

Dan bindiga ya harbe Amurkawa har lahira bayan Trump ya turo sojoji Najeriya

Amma idan amai ya zo da kansa ba tare da an yi sanadin sa ba, to azumi yana nan da ingancinsa.

2. Jinin Haila da na haihuwa

Mata a Musulunci sun samu sassauci lokacin haila da nifasi (jinin haihuwa). Idan mace ta ga jini yayin da take azumi, azuminta ya karye, kuma dole ne ta rama wannan azumin bayan Ramadan.

3. Fitar da maniyyi da gangan

Idan mutum ya fitar da maniyyi da gangan (kamar ta hanyar wasa da al'aura), azuminsa ya ɓaci. Amma idan hakan ya faru ba tare da nufin sa ba (kamar yin mafarki), hakan ba ya ɓata azumi.

A cikin fatawar da ya bayar a shafinsa na YouTube, fitaccen malamin Musulunci, Mufti Menk, ya jaddada cewa wasa da al'aura har maniyyi ya fito, yana karya azumi.

4. Yin jima'i a tsakar rana ana azumi

Ma'aurata da suka yi jima'i a tsakar rana, alhalin ana azumin Ramadan, azuminsu ya karye, kuma za su fuskanci hukunci mai tsanani.

Dole ne wanda ya yi jima'i da tsakar rana ana azumi ya yi kaffara, wanda ya haɗa da ƴanta bawa, ko azumin wata biyu a jere, ko kuma ciyar da matalauta guda sittin idan ba ya da ikon yin sauran.

Kara karanta wannan

2026: Abubuwa 10 da ya kamata Musulmi ya sani kafin fara azumin watan Ramadan

5. Shan taba

A cewar malaman mazhabar Shafi'i, shan taba yana ɓata azumi domin hayaki ne da mutum ke ja da gangan zuwa cikin cikinsa.

A cikin littafin Agar Tak Hanya Lapar dan Dahaga: Panduan Puasa Ramadhan Sehat dan Berkah wanda Iqbal Syauqi Al-Ghifary, Sheikh Sulaiman ya buga, aka wallafa a shafin Cibiyar El Bukhari, an ce shakar hayakin girki ko na hanya wanda ba a iya kauce masa ba ya karya azumi.

6. Yin amai da gangan

Yin amai da gangan yana karya azumi
Wani mutumi yana kokarin yin amai da gangan. Hoto: Peter Dazeley via Getty Images
Source: Getty Images

Amai yana nufin amayar da abinci daga ciki ta baki. Idan Musulmi ya yi amai da gangan, azuminsa ya ɓaci, kamar yadda Dr. Zakir Naik ya sanar a cikin bidiyon da ya wallafa a shafinsa na YouTube.

Amma idan amai ya zo da kansa ba tare da an yi sanadin sa ba, to azumi yana nan da ingancinsa.

7. Ridda

Idan mutum ya fice daga addinin Musulunci (ridda) yayin da yake azumi, azuminsa ya ɓaci nan take. Hakan za ta kasance ne domin imani da Allah shi ne babban sharadi na yin azumi da karɓuwar sa.

Kara karanta wannan

Saudiyya ta sanar da ranar fara azumi bayan ganin watan Ramadan

Malamai sun shawarci Musulmi da su nisanci gulma, kalaman banza, da faɗace-faɗace domin kiyaye ladan azuminsu.

An ga watan Ramadan a Najeriya

A wani labari, mun ruwaito cewa, kwamitin ganin wata a Najeriya ya fitar da sanarwa kan ganin watan Ramadan domin fara azumi a kasar.

Sarkin Musulmi, Muhammad Sa'ad Abubakar III ya tabbatar da ganin jinjirin watan Ramadan a Najeriya a daren ranar Talata 17 ga watan Faburairun 2026.

Sanarwar da aka fitar da kawo karshen watan Sha'aban tare da tabbatar da shiga Ramadan wacce ta kasance mafi girma da daraja a cikin sauran watannin Musulunci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com