Rahoto: An Gano Ayyukan Gwamnatin Tinubu 92 da Aka 'Karkatar da Kudin' a Jihohi 5
- An fara bankado ayyukan damfara a aka fitar da kudadensu a karkashin gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu
- A wani rahoton bibiyar ayyukan raya kasa da aka fitar, an gano muhimman ayyuka 92 da aka sa rashin gaskiya wajen aiwatar da su a jihohi 5
- Rahoton ya kuma tattaro ayyukan da gwamnatin tarayya ta samu nasarar kammalawa, wanda ya hada da shirye-shiryen tallafi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Wani sabon rahoton tabbatar da gaskiya da bin diddigin ayyukan da gwamnatin tarayya ke gudanarwa a ƙarƙashin mulkin Shugaba Bola Tinubu, ya yi tone-tone.
Rahoton ya bankaɗo ayyukan da aka watsar, waɗanda ba a kammala ba, da kuma ayyukan zamba da yawa a karkashin gwamnatin Tinubu.

Source: Facebook
Premium Times ta tattato cewa an saki rahoton bibiyar ayyukan na shekarar 2024/2025 wanda Tracka (shirin sanya idanu na BudgIT) ya fitar a ranar Alhamis.
An bankado ayyukan zamba a mulkin Tinubu
Binciken ya nuna cewa ayyuka 92 na gwamnatin tarayya, waɗanda darajarsu ta kai Naira biliyan 15.07, an aiwatar da su ne ta hanyar zamba.
Haka zalika, rahoton ya gano cewa akwai wasu ɗaruruwan ayyukan da har yanzu ba a kammala ba ko kuma ba a ma fara su ba duk da an sanya su a kasafin kuɗi.
Rahoton ya bayyana cewa ya sanya idanu kan ayyuka 2,760 a cikin jihohi 28, kuma ya gano yadda aka yi zamba a cikinsu wasu, wasu kuma aka yi fatali da su.
Abubuwan da bincike ya gano a jihohi 5
Sakamakon binciken ya nuna cewa ayyuka 1,438 ne kawai aka kammala, ana kan yin wasu 660 yayin da ba ma ba a fara ayyukan 471 ba kwata-kwata, sai kuma 99 da aka yi watsi da su bayan an fara.
Rahoton ya ayyana ayyuka 92 da na damfara saboda karkatar da kuɗaɗen, canza wurin ayyukan ba bisa ka'ida ba, cire kudin ayyukan da an riga an yi a kasafin shekarun baya, rashin kammala aiki, ko kuma yin aiki mara inganci.
Tracka ta bayyana jihohin Imo, Legas, Kwara, Abia, da Ogun a matsayin jihohin da suka fi kowanne yawan irin waɗannan ayyuka n damfara, kamar yadda Tribune Nigeria ta rahoto.
Rahoton ya ce kashi 57.1% na dukkan ayyukan damfarar, waɗanda suka lakume Naira Biliyan 8.61 daga cikin jimillar Naira biliyan 15.07, suna cikin waɗannan jihohi biyar ne.
Ayyukan da gwamnatin tarayya ta kammala
Duk da ƙalubalen da aka fuskanta, rahoton ya nuna wasu ayyuka 15 da suka yi nasara sakamakon matsin lamba daga ’yan ƙasa.
Waɗannan ayyuka sun haɗa da inganta cibiyar kiwon lafiya ta Kaida Sabo, gyaran makarantar firamare ta Nawairudeen a jihar Filato, da kammala asibitin Ikirun.
Sauran sun hada da shirye-shiryen tallafa wa nakasassu a Katsina, da ayyukan kiyaye zaizayar ƙasa a Ribas da rijiyoyin burtsatse a Akwa Ibom.

Source: Twitter
Shugaban Tracka, Joshua Osiyemi, ya jaddada muhimmancin sanya idanu bin diddigin ayyuka gwamnati daga ɓangaren talakawa.
"Idan 5% na 'yan Najeriya za su sa ido kan ayyuka, za a iya kai ga sanya idanu kan kashi 50 na ayyukan ƙasa, wanda hakan zai rage cin hanci da rashawa tare da inganta rayuwar al'umma."
Gwamnatin Tinubu za ta fadada shirin CCT
A wani rahoton, kun ji cewa Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa shirin ta na bayar da tallafin kuɗi (CCT) ya amfani gidaje sama da miliyan 8.3 a fadin Najeriya.
Ministan jin ƙai da rage talauci, Dr Bernard Doro, ne ya bayyana hakan a babban taron ƙasa na farko kan harkokin jin ƙai da aka gudanar a Kuros Riba.
Dr Doro ya ce gwamnati tana da shirin faɗaɗa wannan tallafi domin ya isa ga gidaje miliyan 15 a faɗin ƙasar nan nan da wani ɗan lokaci.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


